Da Ɗumi-Ɗumi: PSG ta lashe Champions League

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Paris Saint Germain ta yi nasarar lashe kofin gasar zakarun Nahiyar Turai, wato UEFA Champions League na kakar 2024/2025.

Hakan ya biyo bayan lallasa Inter Milan ta ƙasar Italiya da ta yi da ci 5 da 0 a wasan ƙarshe.

Wannan shi ne karo na farko da PSG ta taɓa lashe gasar tun bayan kafuwarta a watan Agustan shekarar 1970.

By Babaji