Da ɗumi-ɗumi: ‘Yan bindiga sun kashe ɗan takarar gwamnan jihar Zamfara na APC a 2019

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau

Rahotanni sun nuna cewa wasu mutane da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun harbe dan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC a zaɓen 2019 har lahira a jihar Zamfara akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Rahoton ya ce, lamarin ya faru ne a ƙauyen Rijana da yammacin jiya Lahadi.

Tuni jami’an tsaro suka kai gawar marigayi Sagir Hamidu Gusau asibitin garin Kaduna inda ake sa ran a miƙa gawar ga iyalan mamaci a yau Litinin da safe domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.