
Daga BELLO A. BABAJI
Dakarun atisayen Operation Safe Haven (OPSH) a Jihar Filato, sun halaka wasu mutun biyu da ake zargin ƴan bindiga ne a Gundumar Gimbi dake Karamar Hukumar Wase.
Jami’in Hulďa da Jama’a na tawagar, Manjo Samson Zhakom ya faďi hakan a wata takarda da ya fitar a Jos, ranar Juma’a.
Ya ce, an kashe mutane biyun ne bayan samun rahoton ayyukan ƴan bindiga a yankin.
Manjo Zhakom ya kuma ce sojojin sun yi nasarar kwato wata bindiga kirar AK-47 a yayin atisayen.
Ya kirayi al’ummar jihar da su cigaba da ba su goyon a kokarinsu na dakile ayyukan ta’addanci a jihar, kamaryaddakamfanindillancinlabarai, NAN ya ruwaito.
