Daga AISHA ASAS
Gidauniyar Kannywood ta bayyana farin cikinta tare da taya Aina’u Ade murna bisa naɗin da Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi mata a matsayin Mai Ba da Shawara ta Musamman kan Harkokin Kannywood.
A cikin wata sanarwa da Gidauniyar ta fitar, ta bayyana cewa nadin ya kasance ɗora ƙwarya a mazaunin ta, la’akari da shekaru na gogewa, ƙwazo da kuma manyan gudunmawar da Aina’u Ade ta bayar wajen bunƙasa da haɓaka masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood. Gidauniyar ta jaddada cewa Aina’a Ade ta kasance ɗaya daga cikin fitattun matan da suka yi tasiri a fagen nishaɗi da al’adu, inda ta taka rawar gani wajen ƙarfafa martabar Kannywood a ciki da wajen Jihar Kano.
Sanarwar ta kuma nuna cewa naɗin ya zo a daidai lokacin da ya dace, musamman duba da rawar da mata ke takawa a harkokin mulki da hidimar jama’a. A cewar Gidauniyar, shigar mata masu basira da kwarewa cikin tsarin gwamnati na taimaka wa wajen samar da ra’ayoyi masu faɗi da tsare-tsaren da suka shafi ci gaban al’umma baki ɗaya.
Gidauniyar Kannywood ta bayyana cikakkiyar ƙwarin gwiwa a kan cewa Aina’u Ade za ta bayar da gudunmawa mai ma’ana wajen ci gaba da ɗaukaka Kannywood, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki a masana’antar fina-finai, ciki har da ’yan wasa, daraktoci, masu shirya fina-finai da ƙungiyoyin ƙwararru.
A ƙarshe, Gidauniyar ta yi mata fatan nasara da aiki mai armashi a sabon muƙaminta, tare da fatan wannan dama za ta zama wata babbar kafa ta kawo sauye-sauye masu ɗorewa ga Kannywood da matasan da ke dogaro da ita.
