Daga AMINA YUSUF ALI
Gwamnatin Tarayya ta yi alƙawarin cewa, nan da watanni 10 masu zuwa za ta kammala gini sannan kuma ta buɗe kasuwar gwal ɗin da take ginawa a Jihar Kano.
Ministan tama da ƙarafa na tarayyar Nijeriya, Arc Olamilekan Adegbite, shi ya tabbatar da haka a yayin wata ziyarar rangadi da ya kai ga kasuwar da ake ginawa a halin yanzu a jihar Kano.
Waɗannan jawabai suna ƙunshe ne a cikin wata takarda da kakakin Ma’aikatar tama da ƙarafa, Idowu Jokpeyibo ya wallafa.
A cikin jawabin, an bayyana cewa, Shugaba Buhari na Nijeriya ya yi alƙawarin cewa, tabbas gwamnatinsa za ta kammala ginin kasuwar gwal ɗin wanda a halin yanzu ake kan aikin sa, kafin nan kafin ƙarshen shekarar da muke ciki.
Ministan tama da ƙarafa Arc Olamilekan Adegbite na Nijeriya shi ya bayyana haka a yayin ziyarar rangadi a kasuwar da ake ginawa a Kano.
Ministan ya ƙara da cewa: Wannan wani yunƙuri ne daga ɓangaren gwamnati mai ci, domin ganin an bunƙasa harkar haƙowa tare da hada-hadar duwatsu (masu daraja) domin samar da abin yi a dukkan yankuna guda 6 da muke da su a ƙasar nan. Inda ya bayyana cewa: “Wannan kasuwar Gwal da ake ginawa a ƙaramar hukumar Kumbotso, idan har aka samu nasarar kammala ta, to za ta goga kafaɗu da sauran kasuwannin gwal da suke a faɗin Duniya.
A cewar sa, babban maƙasudin gina kasuwar shi ne, domin a samu damar sarrafa tarin gwal ɗin da Nijeriya take da shi a ƙasar, sannan a samar da ayyukan yi, kuma a samar da kuɗin shiga ga Gwamnatin. Da a ce ana ɗaukar gwal ɗin Nijeriya don sarrafawa a wata ƙasa, to gara a ce a ƙasar ma an samar da wajen sarrafa shi a ƙasar, inji shi.