Har yanzu ba a sabunta wa kamfanin Airtel lasisin zamansa a Nijeriya ba – NCC

Daga UMAR M. GOMBE

Hukumar Kula Sadarwa ta Nijeriya (NCC) ta ce har yanzu ba ta amince da sabunta wa kamfanin sadarwa na Airtel lasisin gudanar da harkokinsa ba a Nijeriya saɓanin iƙirarin da shugaban kamfanin a Nijeriya, Mr. Olusegun Ogunsanya, ya yi.

Daraktan Sahen Hulɗa da Jama’a na NCC, Dr. Ikechukwu Adinde, shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Lahadin da ta gabata.

NCC ta tabbatar da cewa lallai kamfanin Airtel ya aika da takardar neman sabunta lasisin zamansa a Nijeriya, amma hukumar ba ta amince da hakan ba tukuna.

NCC ta ci gaba da cewa an ja hankalinta kan wani rahoto da aka wallafa a intanet inda aka ruwaito Mr. Olusegun Ogunsanya ya ce an sabunta wa kamfanin Airtel lasisin zamansa a Nijeriya na wa’adin shekaru 10 masu zuwa.

An ruwaito Mr. Ogunsanya ya faɗi haka ne a wajen wani taro da kamfanin Airtel ya gudanar a ranar 14 ga Yulin 2021 a jihar Legas.

Lamarin da NCC ta ce ba haka yake ba saboda a cewarta, takardar neman sabunta lasisin da kamfanin Airtel ya miƙa mata tana kan bin matakan da suka dace kafin amincewa da ita.