Kotu ta taka wa majalisar dokokin Zamfara burki kan shirin tsige Mataimakin Gwamna

Wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta dakatar da Majalisar Dokokin Jihar Zamfara daga shirinta na neman tsige Mataimakin Gwamnan Jihar, Mahdi Gusau.

Alƙali Obiora Egwuatu shi ne ya ba da wannan umarni a yau Litinin yayin da yake yanke hukunci kan ƙarar da jam’iyyar PDP ta shigar ta hannun lauyanta, Ogwu Onoja, SAN.

Cikakken bayani na nan tafe.