INEC ta yi kira ga jam’iyyu su daidaita rikicin cikin gida da ya dabaibaye su kafin babban zaɓe

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Hukumar Zaɓen Nijeriya, INEC ta yi tsokaci game da matakan shari’a da ɓangarorin cikin gida na jam’iyyun siyasar ƙasar ke ɗauka a tsakaninsu, da kuma rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyun.

Shugaban Hukumar Zaɓen, Farfesa Joash Amupitan wanda ya bayyana damuwar ya ce yanayin ba alheri ba ne ga jam’iyyun, kuma hakan na yin barazana ga saita tsarin dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Farfesa Amupitan ya koka da cewa, maimakon jam’iyyun su zama wani tsanin kawo sauyi a ƙasa, amma sun koma suna hamayyar shugabanci da ringingimu, al’amarin da ya koma kamar wani wasan kwaikwayo.

Hukumar INEC ta yi kira ga jam’iyyun su gaggauta daidaita rikicin cikin gida da ya dabaibaye su kafin babban zaɓe.

“Zaɓuka na jam’iyyu su ne ginshiƙin gudanar da babban zaɓe, don haka muke kira ga jam’iyyun su yi ƙoƙarin daidaita duk wata matsala ko rashin fahimta da ke tsakaninsu a jam’iyance kafin a kai ga zuwa kotu,” kamar yadda Hajiya Zainab Aminu Abubakar, jami’a a sashen yada labarai da wayar da kan jama’a a hukumar INEC ta shaida wa manema labarai.

Ta ƙara da cewa kotu ce ya kamata a ce ya zama wuri na ƙarshe da za a je domin daidaita duk wata matsala tsakanin jam’iyyu.

INEC ta ce harakar kotu na jefa ta cikin wani ƙalubale musamman idan an samu saɓanin hukunci daga wata kotu zuwa wata.

“Wannan yana wahalar da hukumar zaɓe wajen gudanar da ayyukanta na tunkarar babban zaɓe,” inji Hajiya Zainab Aminu.

Hukumar INEC ta nuna damuwa musamman yadda rikicin cikin gida na jam’iyyu zai iya tasiri ga ingancin zaɓen fitar da ‘yan takara.

Hukumar zaɓe ta ce laifi daga ƙarshe yana dawo wa kanta ne sakamakon riginginmun jam’iyyu musamman idan har an jingine da kotu.

“Laifin da ba na hukumar zaɓe ba, sai ya dawo kanta a musamman lokacin da jam’iyyu suka gabatar da hukunce-hukunce na kotu mabambanta a ƙurarren lokaci.”

“Ko kuma idan an yi hukuncin da bai yi wa wani ɓangare na jam’iyya daɗi ba, daga ƙarshe sai laifin ya daow kan hukumar zaɓe,” in ji Zainab Aminu.

Hukumar INEC ta ce idan jam’iyyun za su yi ƙoƙarin sasanta rikicinsu na cikin gida a jam’iyyance zai taimaka mata wajen shirin gudanar da zaɓe.

Jam’iyyu da dama a Nijeriya na fuskantar rikicin cikin gida inda wasu jam’iyyun ma sun rabe gida biyu.

Yawan zuwa kotu kuma na ɗauke hankalin jam’iyyun musamman a daidai lokacin da ya kamata su a haɗu domin tallata jam’iyya.

A ranar 23 ga watan Afrilu zuwa 30 ga Mayun 2026 ne hukumar zaɓen Nijeriya ta ba jam’iyyu domin fitar da ‘yan takara.

Ranakun babban zaɓen Nijeriya na 2027, kamar yadda hukumar ta fitar su ne:

Zaɓen Shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya: Asabar, 16 ga watan Janairun 2027.

Zaɓen gwamnoni da ‘yan majalisar jihohi: Asabar, 6 ga watan Fabarairun 2027.

Sanarwar da hukumar ta fitar ya ci gaba da cewa “bisa dogaro da sabon jadawalin”, hukumar ta amince da wadannan kwanakin wata domin shirye-shiryen zaben:

Za a gudanar da zaɓen fitar da ‘yan takara, da kuma warware duk wata takaddama da za ta taso a lokacin zabukan, daga ranar 22 ga watan Afrilun 2026 zuwa 30 ga watan Mayun 2026.

Za a fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya daga ranar 19 ga watan Agusta 2026.

Yaƙin neman zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi zai fara daga ranar 9 ga watan Satumban 2026.

By ukarofi