Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
Rikicin da ya ke ta ci gaba da girgiza jam’iyyar PDP ya sake tsananta bayan ficewar wasu manyan gwamnoni guda shida tun bayan zaɓen 2023, lamarin da ya haifar da muhawara mai zafi a fagen siyasar Nijeriya.
Daga Siminalayi Fubara zuwa Ademola Adeleke, jerin sunayen jagororin da suka ja daga ya nuna irin girman matsalar da jam’iyyar ke fama da ita a matakin ƙasa.
A makonnin baya ne Gwamna Sim Fubara na Jihar Ribas da Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun suka zama sababbin shugabannin da suka rabu da PDP, abin da ya tayar da ƙura a tattaunawar siyasa a faɗin ƙasar nan.
Fubara ya tsallaka zuwa jam’iyyar APC tare da goyon bayan manyan jakadu da wasu ‘yan majalisa goma sha shida daga majalisar dokokin Ribas.
Yayin jawabin sanarwar sauyawar sa, Fubara ya ce ba zai iya mara wa Shugaba Bola Tinubu baya ba idan bai “fito fili” ya jingina da jam’iyyar shugaban ƙasa kai tsaye ba.
Shi kuwa Adeleke, ya rubuta takardar barin jam’iyyar PDP ne ta hanyar kakakinsa, inda ya danganta wannan mataki da rikicin cikin-gida da ya dabaibaye shugabancin jam’iyyar a matakin ƙasa. Daga nan sai ya tafi zuwa jam’iyyar Accord domin neman tazarce.
A Bayelsa kuwa, Douye Diri ya sanya PDP a baya bayan dogon tarihi da ya shafe a cikinta. Diri wanda aka karɓe shi cikin jam’iyyar APC a gaban Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce wannan sauyi ba nasa ba ne kaɗai, “amma na al’ummar Ijaw gaba ɗaya.” Shiga APC da ya yi ya zo tare da cikakken goyon bayan ‘yan majalisar dokokin jiharsa.
Haka zalika, Gwamna Peter Mbah na Enugu ya sanar da ficewarsa cikin wani jawabi na kai tsaye a talabijin, yana mai cewa lokaci ya yi da zai “yanke shawarwarin da za su sake tsara makomar jihar Enugu.” Ya bayyana komawa APC a matsayin mataki na ceto makomar jihar.
A Delta, Mubayyacin Gwamna Sheriff Oborevwori ya yi watsi da PDP a watan Afrilu 2024, bayan wani taro na manyan jiga-jigan jam’iyyun siyasa. Masu lura da siyasar Delta na ganin sauyawar tasirin Oborevwori wani ginshiƙi ne na gina matsayi ga APC gabanin 2027.
Sai kuma Gwamna Umo Eno na Akwa Ibom wanda shi ma ya tsallaka zuwa APC a ranar 6 ga Yuni 2025, yana mai cewa yana shiga jam’iyyar ne “daga matsayi na ƙarfi, ba rauni ba,” domin ya mara wa sauye-sauyen tattalin arzikin gwamnatin Tinubu baya.
Sauye-sauyen gwamnoni guda shida cikin lokaci kaɗan na nuna irin yadda tasirin APC ke ƙaruwa, tare da yadda PDP ke ci gaba da fama da matsalolin shugabanci da rashin daidaito cikin gida. Masu nazari na ganin wannan na iya zama muhimmin al’amari da zai yi tasiri sosai a faifan siyasar 2027.
