Kalaman jarumin Kannywood, Sadiq Sani na fifita shugaban Nijar akan Tinubu sun tayar da hazo a kafar sada zumunta

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Sanannen jarumin masana’antar Kannywood, Sadiq Sani Sadiq ya haddasa cece-kuce a kafar sada zumunta bayan fifita Shugaban sojin ƙasar Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani akan Shugaba Bola Tinubu na Nijeriya.

Rahotanni sun bayyana cewa, jarumin ya furta kalaman ne a wajen wani taron jama’a a Nijar, inda ya gabatar da jawabin da ya karaɗe kafafen Soshiyal Mediya.

Da yake jawabi ta harshen Hausa, Sadiq ya jinjina wa Janar Tchiani wajen bayyana shi a matsayin jagora mai kishi da ke son ƙasarsa, mutanensa da kuma Nahiyar Afirka.

“Na fi son Shugaban Nijar akan Shugaba Bola Tinubu. Me ya sa na faɗi haka? Saboda, a zuciyata na san yana son Afirka da ‘yan Afirka. Yana son mutanensa kuma yana alfahari da asalinsa,” inji jarumi Sadiq.

Ya kuma yaba wa Tchiani bisa ƙoƙarinsa na ɗaukaka darajar Afirka da ikonta a idon duniya, lamarin da ya sa al’umma da dama suke goyon bayansa.

Haka kuma, jarumin ya ƙara da cewa ya fi ganin yana da kusanci da mutanen Nijar akan waɗanda suke ‘yan kudancin Nijeriya ne.

Waɗannan kammala da jarumin ya watsa a bainar jama’a sun tayar da hazo musamman a kafafen sada zumunta, inda wasu ke ganin su a matsayin waɗanda suke wakiltar jarumin shi kaɗai musamman ganin yadda suke da alaƙa da al’ada yayin da wasu ke ɗaukar su matsayin dalilan haddasa rarrabuwar kai acikin ƙabilun Nijeriya.

By Babaji