Ƙungiyar National Progressives Councillors’ Forum (NPCF), wadda ke wakiltar kansiloli 10,378 na jam’iyyar APC a faɗin Najeriya, ta yi kira ga Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya umarci hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa da na tsaro na tarayya su dakatar da duk wani bincike ko mataki da ake ɗauka kan koke-koken da ƙungiyar ta bayyana a matsayin marasa tushe kuma masu ɗauke da manufofin siyasa kan Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sakkwato.
A wata sanarwa da aka fitar bayan taron kwata-kwata na shiyyar Arewa maso Yamma da aka gudanar a Kano, NPCF ta yi Allah-wadai da abin da ta kira yaƙin ɓata suna da hare-haren kafafen yaɗa labarai da ke danganta Sanata Yari da kama ɗanyen zinari na naira biliyan 4.4 a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano a ranar 11 ga watan Yuni. Ƙungiyar ta ce Hukumar EFCC ta bayyana sunayen waɗanda ake zargi da hannu a lamarin, kuma babu sunan Sanata Yari a cikinsu. Haka kuma, ta musanta zarge-zargen da ke cewa yana ɗaukar nauyin zanga-zangar adawa da gwamnati ko kuma tallafa wa jam’iyyar ADC.
Ƙungiyar ta yabawa irin gudunmawar da Sanata Yari ya bayar a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara da kuma shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya. Ta ce a matsayinsa na mai wakiltar Zamfara ta Yamma a Majalisar Dattawa, babu wata shari’ar cin hanci ko laifi da ke kansa a kotu. NPCF ta kuma ce mulkinsa ya samar da shirin sulhu da afuwa na farko a jihar, gina filin jirgin sama, hanyoyi, cibiyoyin ilimi da kuma jami’ar farko mallakar gwamnatin jihar a Gusau.
Bugu da ƙari, ƙungiyar ta zargi wasu ’yan siyasa daga Arewa maso Yamma da suka kasa samun tikitin takarar gwamna da amfani da muƙaman gwamnati wajen tsoratarwa da matsa lamba ga Sanata Yari. NPCF ta bayyana cewa irin waɗannan matakai na iya kawo cikas ga haɗin kan APC da kuma manufar “Renewed Hope”. Ta kuma yi kira ga gwamnatin Jihar Zamfara da sauran masu ikirarin biyayya ga APC su daina abin da ta kira aiki da ke cin karo da muradun jam’iyyar.
A ƙarshe, NPCF ta sake jaddada goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Tinubu, amma ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ba ta ɗauki matakin dakatar da abin da ta kira zarge-zarge marasa tushe, tsoratarwa da kuma yaƙin ɓata suna kan Sanata Abdul’aziz Yari ba, ƙungiyar za ta sake nazarin matsayinta da tsarin goyon bayan da take bai wa jam’iyyar APC.
