Kotu ta soke umarnin kama Turaki, shugaban tsagin PDP

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Wata Babbar Kotun Abuja a ranar Laraba ta soke umarnin kamawa da ta bayar a ranar 26 ga Maris domin cafke shugaban jam’iyyar PDP na wani ɓangare, Kabiru Turaki.

Mai shari’a Peter Kekemeke ya soke umarnin kama ne yayin da yake yanke hukunci kan roƙon baki da lauyan Turaki, Chris Uche SAN ya gabatar, bayan bayyanar Turaki a kotu.

Da aka kira shari’ar, Uche ya nemi afuwar kotu kan rashin halartarsa a ranar da ta gabata.

Mista Uche, wanda ya ce yana waje ne a ƙasar, ya bayyana cewa ya dawo ne da safiyar ranar kuma ya nufi kotu kai tsaye.

Ya kuma nemi afuwa a madadin wanda yake ƙarewa, yana mai cewa shi Babban Lauya ne (SAN) kuma yana da matuƙar girmamawa ga kotu.

Ya ce rashin halartar Turaki a ranar da ta gabata ba da gangan ba ne, kuma bai yi nufin raina kotu ba.

Mista Uche ya ce don nuna gaskiya, zai janye buƙatar da ya gabatar a madadin wanda yake karewa ta neman dakatar da aiwatar da umarnin kama.

Ya ƙara da cewa Mista Turaki a shirye yake ya karɓi tuhumar da ake yi masa a kotu.

Da yake mayar da martani, lauyan masu ƙara, Usman Rabiu, ya ce ba shi da adawa da buƙatun Uche.

Mista Rabiu ya bayyana cewa manufar bayar da umarnin kama ita ce tilasta wanda ake tuhuma ya bayyana a kotu.

Ya ƙara da cewa tun da ya halarci kotu, manufar umarnin ta cika.

“Tunda ya (Turaki) zo kotu, ba mu da wata adawa da gurfanar da shi yau.”

A hukuncinsa, Mai shari’a Kekemeke ya lura cewa wanda ake tuhuma ya halarci kotu da kansa kafin a aiwatar da umarnin kama.

Alƙalin ya kuma lura cewa lauyansa ya nemi afuwa kan rashin halartarsa, duk da cewa dalilin rashin halartar bai fito fili ba daga abin da Uche ya bayyana.

Sai dai ya zaɓi yafewa wanda ake tuhuma tare da soke umarnin kama.

Mai shari’a Kekemeke ya ce tun da an tsara sauraron buƙatar da wanda ake tuhuma ya gabatar a ranar Laraba, bai dace a ci gaba da gurfanar da shi ba a wannan lokaci.

Har ila yau, alƙalin ya goge buƙatar da Turaki ya gabatar, inda ya nemi a dakatar da aiwatar da umarnin kama, bayan da Uche ya nemi janye ta kuma Rabiu bai nuna adawa ba.

Daga nan, Mai shari’a Kekemeke ya ɗage shari’ar zuwa ranar 22 ga Afrilu domin gurfanar da Turaki kan tuhuma guda ɗaya mai lamba: CR/647/2026 da Babban Sufeton ‘Yan Sanda (IGP) ya shigar a kansa.

A ranar 26 ga Maris ne Mai shari’a Kekemeke ya bayar da umarnin kama Turaki bayan da ya gaza halartar kotu domin gurfanar da shi kan tuhuma guda ɗaya ta aikata laifi, inda ake zarginsa da, a cikin wasu abubuwa, bayar da bayanan ƙarya ga ‘yan sanda.

By ukarofi