
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Hedikwatar Tsaro DHQ, ta sanar da cewa kwamandan ISIS da sojojin Amurka da Nijeriya suka halaka a kwanan nan, wato Abu Bilal Al-Manuki, na da hannu a garkuwa da ɗalibai mata na makarantar Dapchi a Jihar Yobe.
Daraktan yaɗa labaran hedikwatar, Manjo-Janar Samaila Uba ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar a Abuja.
A cewarsa, atisayen da ya yi ajalin Al-Minuki ya gudana ne ta hanyar rarraba bayanan sirri da haɗin-gwiwa tsakanin dakarun tsaron Nijeriya da na Amurka.
Ya bayyana marigayin ɗan ta’addan a matsayin babban jigo a harkokin ISIS kuma ɗaya daga cikin kwamandodin da suka fi yi wa tafiyarsu hidima.
Uba ya ce, atisayen ya alamta samun babban nasara a yaƙi da ta’addanci a Nijeriya, yankin Tafkin Chadi da kuma shiyyar Sahel da dakarun tsaro ke yi.
Ana ɗaukar marigayin jigon a matsayin ɗan ta’adda mafi aiki a duniya, wanda ya ƙware wajen shirya ƙaddamar da hare-hare da bayar da umarnin garkuwa da mutane.
Al-Manuki na ɗaya daga cikin mayaƙan ISIS da ke aiki tsakanin ƙasa-da-ƙasa a fannin yaɗa labarai da samar da kuɗaɗe da kuma ci-gaba a harkokin samar da makamai, ababen fashewa da tankunan yaƙi, kamar yadda kakakin sojojin ya bayyana.
Kazalika, Uba ya ce Al-Minuki shi ne wanda ya shirya jigilar mayaƙa zuwa Libiya tsakanin shekarun 2015 da 2016, yana mai cewa gabanin haka, shi ɗin sanannen mamban Boko Haram ne.
