
Daga BELLO A. BABAJI
Kwamitin kula da lamuran shugaban Jihar Ribas na Majalisar Wakilai ya dakatar da yin zama da Jagoran jihar, VM Ibok-Ete Ibas (mai ritaya).
A ƴan kwanakin nan ne majalisar ta gayyaci Ibas bisa jagorancin da Shugaba Bola Tinubu ya ɗora masa a jihar bayan sanya dokar ta-ɓaci.
Mai magana da yawun majalisar, Sakin Rotimi ya bayyana hakan a wata takarda.
Ya ce, sun yi haka ne da nufin zaɓar wata ranar don kammala wasu shirye-shirye da ke da alaƙa da zaman tattaunawar.
Majalisar ta ƙafa kwamitin mutane 21 da za su sanya ido kan harkokin shugabancin jihar a ƙarƙashin jagoran.
