Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano
Makarantar Al-Azaha a jihar Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai da raba kyautuka ga waɗanda suka yi ƙwazo a yayin taron a harabar makarantar ranar Asabar da ya samu halartar ɗinbin iyaye da sauran manyan baƙi.
A bayanan su game da taron, Daraktocin makarantar Farfesa Binta Tijjani Jibrin da Farfesa A’ishatu Abdu Isma’il da suka kafa makarantar sun bayyana irin ɗinbin gudunmuwa da makarantar ke bayarwa ga bunƙasa cigaban ilimi.
Farfesa A’ishatu Abdu Isma’il ɗaya daga daraktocin ta bayyana cewa taron ana shirya shi ne kowace ƙarshen shekara na zangon karatu, saboda a ƙarfafa gwiwar sauran yara domin su a makarantar Al-Azhar abinda suka fi ƙarfafawa shine koyar da yara su zama masu amana da Iklasi shine ya sa suke koyawa yara karatu da tarbiyya sosai na addinin musulunci.
Ta ƙara da cewa suna ƙoƙarin cusa tarbiyya ga ɗalibai ta hanyar dora akan tsayawa akan gaskiya shi yasa ma ba su yarda da satar amsar jarabawa ba a makarantar duk abinda ake gani na kwazon ɗaliban su, haka yake haka aka koya musu, kuma ana samun nasara,tun daga kafa makarantar suna bibiyar ɗaliban su da kyau waɗanda suka je jami’o’i da manyan makarantu bayan sun gama sukan samu ɗalibai na zama kan gaba a masu kwazo a ajin su
Farfesa A’ishatu Abdu Isma’il ta ce ana samun ɗaliban da suka fito daga makarantar sun gama jami’a ko manyan makaranta da sakamako mai kyau yawancin su wasu sun zama likitoci ,lauyoyi injiniyoyi da manyan ma’aikata a wurare da yawa kuma ana samun su da kwazo da tarbiyya da rikon Amana a duk inda suka sami kansu.
Ita ma a nata bayanin Farfesa Binta Tijjani Jibrin ta ce in ana maganar tarbiyya, mutunci da riƙon amana ana samun sune ta tushen koyarwar addinin musulunci a matsayin su na musulmi domin shine ginshiƙi don haka ganin ilimi na zamani abu ne mai muhimmanci shi yasa suke gyara inda suka ga wani abu da bai dace da tarbiyya ba a ciki sai su cire duk wani abu da zai ɓata tarbiyya sannan su kawo abinda ya dace su koyawa ɗalibansu wannan ta sa suke haɗa ilimin addini dana zamani a makarantar.
Ta ce tunda aka kafa makarantar shekara ta 2000 sun ɗauki ilmi da bayar da tarbiyya a matsayin haƙƙi ne na iyayen yara da malamai da makaranta don haka ake haɗa hannu don tabbatar da.tarbiyya suna da hanyoyi da yawa da suke shigo da iyaye a cikin harkokin makarantar domin su taya su wannan aiki, suna kuma samun goyon bayan iyayen yara kashi 90 bisa 100.
Farfesa Binta Tijjani Jibrin ta ce suna da tsare- tsare na tallafawa ya’yan malamai dana ma’aikatan makarantar da ya’yan al’ummar da suke maƙotaka da makarantar suna kuma da tsarin tallafawa wasu makarantun Gwamnati da suke kusa dasu ta hanyar horar da malamansu da tallafi ga makarantun suna baiwa yara masu kwazo da iyayensu basu da hali tallafin kudin makaranta “scholarship”
Farfesa Binta Tijjani Jibrin ta yaba matuƙa da irin goyon baya da gudunmawa da iyaye da malaman makarantar suke bayar wajen kulawa da ɗaliban da hakan na taimakawa wajen fice samar da makarantar ta ke wajen bada ingantaccen ilimi ga ɗalibai
Shi ma shugaban kwamitin iyaye da malamai na makarantar Al-Azhar.Alhaji Ibrahim ɗanyaro, shugaban Dattawan Kasuwannin Sabon Gari da Singa yace suna farin ciki da taron yaye ɗaliban domin rana ce da makarantar ke nuna ta kai matsayinda yakamata a wajen bayar da tarbiyya da bada ilimi.
Ya ce Makarantar da farko ta yi suna ne wajen bada ilimin zamani amma yanzu tana ƙoƙarin haɗawa da ilimin addinin Musulunci wanda dama shine abinda ya kamata a samu ‘ya’yan Musulmi a kai su zama ‘yan boko kuma masana akan addini ta wannan za a ci riba biyu an haɗa ilimi biyu da zai amfanar da al’umma.
