Mun shiga mawuyacin hali yayin da ta’addanci ke mamaye jiharmu, inji Gwamnan Benue

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Gwamnan Jihar Benue, Hyacinth Alia ya bayyana cewa jihar tana kewaye da ƴan ta’adda da ƴan fashi, inda hare-haren da ake kai wa a ƙauyuka a ƴan kwanakin nan sun kere tsakanin makiyaya da manoma.

An samu adadi mai yawa na hare-hare a ƴan makonnin nan a yankin Arewa ta Tsakiya, waɗanda suka jefa ƙananan hukumomi da dama cikin mawuyacin hali, lamarin da a sakamakonsa aka rasa mutane masu tarin yawa.

A yayin hira da shi ta gidan talabijin na Channels a ranar Juma’a, Gwamna Alia ya ce ƴan ta’addar sun shirya hare-haren ne tare da ƙaddamar da su a wurare mabanbanta a jihar.

Ya ce, lallai waɗannan hare-haren sun wuce a ce na manoma da makiyaya ne kaɗai, inda ƙwararrun mayaƙa ne suke aiwatar da su.

Ya kuma ce, abin takaicin shine ba a taɓa ko ɗaya daga cikinsu ba saboda a mafi yawancin lokuta su kan kai hari ne da tsakiyar dare, inda cikin hanzari suke tserewa.

Gwamnan ya zargi wasu ƴan majalisar ƙasa da ɗaukar nauyin hare-haren da ke faruwa a Benue, yana mai cewa lallai ba za su lamunci hakan ya cigaba da aukuwa ba.

Ya kuma ce, wani rahoton da tawagar shari’a ta ke gudanarwa a jihar ya ayyana sunayen wasu manyan mutane, inda da zara an kammala shi a mako mai zuwa, za su ɗauki matakin doka a kai.

By Babaji