Muna gina titinan da za su yi shekaru 100 ba su yi komai ba – Gwamnatin Tinubu

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja 

Ministan Ayyuka na Nijeriya, Mista Daɓe Umahi, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba wai gina titina ba ce kawai, a’a, tana gina ababen more rayuwa da aka tsara na tsawon ƙarni.

Mista Umahi ya bayyana haka ne a ranar Larabar da ta gabata, yayin da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ya duba aikin sake gina babbar hanyar Legas-Sagamu-Ijebu-Ode-Benin da ake yi.

Ministan ya bayyana cewa, amfani da fasahar kwalta na siminti wajen gina titinan shine don tabbatar da ɗorewa da inganci idan aka kwatanta da kwalta.

Ya ce babu wata hanyar kwalta da ta kai shekaru 50.

“Ku nuna min duk wata titin kwalta a ƙasar nan da ta shafe shekaru 50. Hatta titin Legas zuwa Ibadan tuni ya lalace a wasu sassa.

“Amma titi na siminti da aka gina a jihar a shekarun 1950 na nan a tsaye.

“Ba wai kawai muna gina titina ba ne; muna gina hanyoyin da za su ɗauki sama da shekaru 100”, inji Ministan.

Ya bayyana jin daɗinsa da sauri da ingancin aikin aikin sake gina titina, inda ya bayyana shi a matsayin wani abin koyi na sabon tsarin samar da hanyoyin tarayya a Nijeriya.

Ministan wanda ya jagoranci tawagar binciken zuwa sashe na 1 da na 2 na aikin, ya ce ɗan kwangilar ya kammala kusan kilomita 8.1 na titin ɗaya titin Sagamu tare da aiki “dare da rana” don cika wa’adin watan Disamba.

“Wannan aikin wani kari ne na shirin Shugaban ƙasa na Bunƙasa Kasafin ƙasa (PIDF) a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Tinubu,” inji shi.

Daga nan ya umarci mai kula da ayyuka na tarayya a Ogun da ya tabbatar da cewa duk wani tsayin kilomita 5 da aka kammala an buɗe wa zirga-zirga bayan kwanaki 21 kuma an kula da shi yadda ya kamata don sauƙaƙa zirga+zirga da rage damuwa na tafiye-tafiye ga masu ababen hawa.

Dangane da abubuwan da suka shafi ƙayyadewa da tsaro na aikin, ya ce babbar hanyar za ta ƙunshi fitilun titi masu amfani da hasken rana, da na’urar ɗaukar hoto ta CCTɓ, wuraren hutawa, dakunan shan magani, wuraren tsaro, wuraren cin abinci, da sauran kayayyakin da ke gefen titi a ƙarƙashin shirin bunƙasa babbar hanya (HDMI).

“Har ila yau, muna gabatar da dashen itatuwa a kan titin don kyawun muhalli da kariya.

Ya ƙara da cewa “A farkon makon farko na watan Nuwamba, ya kamata ‘yan Nijeriya su fara ganin na’urorin samar da hasken rana da sauran abubuwan da ke faruwa.”

Ministan ya jaddada ƙudirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan titina a kan lokaci, inda ya gabatar da cewa tsarin samar da ababen more rayuwa na Tinubu ya ba da fifiko ga inganci, aminci, da kimar dogon lokaci.

Daga baya Mista Umahi ya jagoranci tawagarsa domin duba aikin gyaran gadar sama da ta lalace a ƙauyen Alapako, daura da babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya ya ruwaito cewa, ministan ya kuma duba aikin da ake yi a yankin Ojoo na jihar Oyo.

By ukarofi