NiMeT ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a faɗin Nijeriya ranar Laraba zuwa Juma’a

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Hukumar Kula da Yanayi ta Ƙasa, NiMeT, ta yi hasashen samun hasken rana da hadari mai ɗauke da tsawa daga ranar Laraba zuwa Juma’a a sassan Nijeriya.

A hasashen nata na ranar Talata, NiMeT ta yi nuni da cewa, za a samu hasken rana a ranar Laraba a yankin Arewa.

Haka kuma, za a samu hadari da tsawa a lokutan rana da yamma a yankunan Jihohin Kaduna, Adamawa, Sakkwato, Kebbi, Zamfara da Taraba.

A Jihohin Abuja, Benue, Kwara, Neja, Filato da Kogi kuwa, za a samu hadari da yiwuwar tsawa a lokacin rana da kuma yammaci.

A kudancin ƙasa kuwa, za a samu hadari mara ƙarfi a Jihohin Delta, Kuros-Riba, Akwa-Ibom, Ribas da kuma Bayelsa a lokacin safiya.

NiMeT ta kuma yi kira ga al’umma da su kiyaye musamman a wuraren da ake sa ran samun ruwan sama mai ɗauke da iska da tsawa yayin da suke shirya gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

By Babaji