Sojoji sun bindige DPO a Zamfara

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

Rahotanni daga jihar Zamfara sun bayyana cewa, wani soja ya harbe wani mai suna Halliru Liman wanda DPO ne na ƴan sanda da ke aiki a ofishin Wasagu, a wata matsaya ta bincike.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, ASP Yazid Abubakar ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da jami’in ƴan sandan ke kan hanyarsa ta zuwa Birnin Kebbi a jihar Kebbi don halartar wani taro inda wani soja wanda ɗaya ne daga cikin tawagar atsayen Hadarin Daji ya tare shi a yankin Ɗanmarke da ke ƙaramar hukumar Bukuyum.

Ya ce, an kashe jami’in duk da cewa ya bayyana kansa a matsayin ɗan sanda.

Rundunar ƴan sandan ta buƙaci a zurfafa bincike game da lamarin don tabbatar da kamo waɗanda ke da hannu a ciki tare da hukunta su.

Kazalika, rundunar ta aika da saƙon ta’aziyyarta ga ahalin mamacin tare da yi mu su alƙawarin yin adalci akan haka.

By Babaji