Trump ya yi barazanar ƙaƙaba harajin kashi 25 kan wayoyin iPhone

Spread the love

Shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar ƙaƙaba harajin kashi 25 kan wayoyin iPhone da ba a ƙera a cikin ƙasar ba.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Trump ya ce yana son ganin an riƙa ƙera wayoyin a Amurka, ”ba Indiya ko wani wuri a duniya ba’.

Tuni dai hannayen jarin kamfanin Apple ya fara sauka.

Kamfanin na Apple ya zaɓi Indiya a matsayin wurin da zai riƙa ƙera wayoyinsa domin kauce wa harajin Chana.

Trump ya daze yana buƙatar Apple ya gina iPhone, samfurinsa mafi muhimmanci a Amurka.

Masana sun yi ikirarin cewa hakan na buƙatar saka hannun jari mai yawa kuma zai sa wayoyi su yi tsada sosai.

A ƙarƙashin jagorancin Cook, Apple ya gina hanyoyin samar da kayayyaki a Asiya a cikin ‘yan shekarun da suka gabata tare da manyan masana’antu, musamman a ƙasar Chana.

A cikin ‘yan shekarun nan, kamfanin ya kuma haɓaka samar da kayayyaki a Indiya da Vietnam, a wani ɓangare na mayar da martani ga illar kullen annobar Koroba a Chana.

By ukarofi