
Daga BELLO A. BABAJI
Hukumar Kula da Birnin Tarayya (FCTA) ƙarƙashin jagorancin Ministan Abuja, Nyesom Wike ba ta buɗe Hedikwatar Jam’iyyar PDP ba duk da umarnin Shugaba Bola Tinubu.
A ranar Litinin ne jami’an FCTA suka fara rufe filaye da gine-ginen da ba a biya musu kuɗaɗen hayar ƙasa ba wato ‘ground rent’.
A watan Maris, 2025 ne Wike ya ƙwace filaye 4,794 a birnin tarayyar.
Akan haka ne Shugaba Tinubu ya umarci a dakatar da ɗaukar matakin inda ya nemi a ba su wa’adin kwanaki 14 na su biya kuɗaɗen bashin hayar da ake bin su, kamar yadda Daraktan kula da filaye, Chijioke Nwankwoeze ya tabbatar a wata takarda.
Ya ce, kuɗaɗen sun kai na tsawon shekaru daga 10 zuwa 42, lamarin da ya sa aka ƙwace su.
An ga yadda wasu ma’aikatan jam’iyyar ke zaune a wajen ofishin yayin da wasu kuma suka fake a wasu wurare.
