‘Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa da garkuwa da matarsa da ƴaƴansa a Abuja

Spread the love

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI

Wani ɗan-kasuwa a garin Ushafa na ƙaramar hukumar Buwari da ke Abuja ya rasa ransa a lokacin da wasu ƴan ta’adda suka kai hari gidansa a ranar Alhamis.

Rahotanni sun bayyana cewa, ƴan ta’addan sun yi nasarar yin garkuwa da matarsa da ƴaƴansa a yayin farmakin.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ƴan sandan Abuja, SP Josephine Edeh ta tabbatar da aukuwar lamarin inda ta ce su na gudanar da bincike a kai wajen ceto matar da ƴaƴan mamacin.

Garin Ushafa wani yanki ne da ƴan bindiga ke kai hare-hare a ƴan kwanakin nan.

By Babaji