
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Shugaba Bola Tinubu ya sake wa Jami’ar Maiduguri suna, inda ya sanya mata sunan marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.
Shugaban Ƙasar ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis, yayin Zaman Majalisar Zartarwa (FEC) da aka faɗaɗa don karrama tshohon shugaban a Fadar Shugaban Ƙasa dake Abuja.
Daga yanzu, za a riƙa amfani da “Muhammadu Buhari University’ a matsayin sunan jami’ar.
Zaman ya samu halartar ƴaƴan tshohon shugaban ƙasar duba da gayyata ta musamman da suka samu daga fadar shugaban ƙasar.
