
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
‘Yan bindiga sun halaka wani babban jami’i na Kwalejin Ilimi da ke Maru, Malam Bashar Sani, lamarin da ke ƙara nuna taɓarɓarewar harkar tsaro a ƙauyukan Jihar Zamfara, inda iyalai ke biyan maƙudan kuɗaɗen fansa domin ceto ‘yan uwansu amma duk da haka suke rasa su.
Bincike da dama sun nuna cewa, marigayin ya biya kusan Naira miliyan 25.7 a matsayin fansa da wasu ababen da ‘yan bindigar suka buƙata domin sako mambobin iyalansa da aka sace, kana daga bisani ‘yan bindigar suka halaka shi.
Wasu daga cikin iyalansa da majiyoyin yankin sun ce al’amarin ya fara ne tun tsawon shekaru da dama a lokacin da ‘yan bindiga suka yi awon-gaba da matan jami’in biyu daga garinsu na Tsohon Tasha da ke Ƙaramar Hukumar Maru. Ganin haka ya sa ya tura musu Naira miliyan biyu wajen sako iyalan nasa.
Bayan watanni, ‘yan bindigar suka sake dawowa tare da yin garkuwa da ƙaninsa mai suna Hassan Sani, lamarin da ya tilasta wa iyalan biyan miliyan 3.5 wajen sako shi.
Akan haka ne iyalan suka yi ƙaura zuwa Shiyyar ‘Yan Hudu da ke cikin garin Maru domin samun mafaka. A nan suka zauna na tsawon watanni 18 ba tare da fuskantar irin matsalar ba.
Ana nan, sai ‘yan bindigar suka gano inda suke, wanda ya sa suka kai sabon hari da ya yi sanadiyyar yin garkuwa da Bashar Sani da ɗaya daga cikin matan nasa da aka sace a baya, ‘yarsa da kuma wasu mazauna yankin da dama. A yayin haka sun kuma halaka matar ɗan sanda da tafiya da ‘ya’yanta biyar.
Bayan haka ne ‘yan bindigar suka nemi a biya miliyan N20 domin sako Sani da ‘yan gidan nasu. A cewar makusantansa, an biya cikakken kuɗin fansar.
Bugu da ƙari, masu garkuwar sun nemi a kai musu babura, katin waya na kimanin N200,000 da wayoyin hannu huɗu, waɗanda dukkansu an kai musu. Saidai duk da haka sun cigaba da gabatar da wasu buƙatu.
Bayan haka sun sako sauran iyalan ba tare da jami’in kwalejin ba, wanda bincike ya nuna cewa ya rasu ne a hannun ‘yan bindigar sakamakon lallasa shi da suka yi da ya haifar masa da munanan raunuka.
