Ƙoƙarin Gwamnatin Kano na inganta ilimi ya sa ta ba mu aikin kujeru – Ƙungiyar Kafintoci

Spread the love

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano

Ambasada Alhaji Nafiu Nuhu, Shugaban ƙungiyar Gandun Albasa ‘general furniture’ ya bayyana cewa Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf ta ba su aikin gudanar da dubban kujeru na zaman ɗalibai da malamai da za a sa a dukkan makarantun jihar.

Ya ce, wannan gagarumin aiki da gwamnati ta ɗauko ya nuna jihar Kano tayi nasarar samun  nagantaccen shugaba jajirtacce da zai tsaya ya dubi matsalolin al’umma ya share musu kuka  wannan shine shugabanci nagari.

Ya ƙara da cewa, kwanakin baya ya ayyana dokar ta ɓaci akan ilimi duk wanda yake Kano zai ga irin dubban kujeru da Gwamnati tasa kafintoci suka yi da za’a raba makarantu a dukkan ƙananan hukumomi 44 wannan kuwa ya samo asali ne bisa koyi da gwamna yake da jagora injiniya Rabiu Musa Kwankwaso domin lokacin da yayi Gwamna ya jajirce wajen inganta ilimi.

Ya ce, babu wata gwamnati da aka yi a jihar Kano da ta samar da kujeru masu yawa a makarantu kamar wannan Gwamnati ta Abba Kabir Yusuf tayi alƙawarin kowace makaranta a Jihar Kano sai an cika ta da  abin zama sai an nemi ɗalibi mai zama a ƙasa an rasa ga littattafai ana rabawa da kayan makaranta domin cigaban al’umma ya dogara ne ga ilimi.

Ambasada Nafiu ya ƙara da cewa ita wannan gwamnati tana kai kowane irin aiki ne ga  ahalinta  su kafintoci na jihar Kano taga sune ya cancanta a baiwa aikin yin kujerun aka basu wannan ya taimaka wajen rage zaman banza da rashin ciniki da sama da mutum 11,000 ne suke  amfana da yin aikin.

Ambasada Alhaji Nafiu Nuhu shugaban ƙungiyar Kafintocin na Gandun Albasa  ya ce  yanzu an soma da yin kujeru sama da  Dubu 50 kuma za a cigaba da yi har sai an wadata dukkan  malarantu  a  jihar Kano da kujerun zama. ya  kuma godewa  Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa wannan dama da ya basu suna yi masa fatan nasara a dukkan abinda yasa a gaba.

By ukarofi