Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya shaida wa masu aniyar zuba jari na ƙasar Faransa cewa ƙofar ƙasar nan a buɗe take don harkokin kasuwanci, yana mai cewa gwamnatinsa na samar da yanayin da za su ci gaba.
Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin wata ganawa da ya yi da Shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron a fadar Elysee.
“Mun kasance muna aiki don daidaita tsarin tsaro a Nijeriya kuma muna ƙara samun masara,” in ji Tinubu.
“A yanzu muna samun ci gaba a fannin tsaro. Zan iya tabbatar wa duk masu zuba jari cewa Nijeriya a buɗe take don kasuwanci.
“Muna tabbatar muku da tattalin arzikin kasuwa mai ‘yanci; mai sauƙi a ciki, babu shamaki,” in ji Tinubu.
Shugaban Nijeriyar ya jaddada matasan ƙasarsa da suka kware, masu ilimi, kuma a shirye suke a basu horo a wani bangare na dalilan da ya kamata masu zuba jari na Faransa su kalli ƙasar da ke yammacin Afirka.
“Muna da ƙwararrun matasa waɗanda ke da ilimi, ƙwararru, kuma a shirye muke a horar da su don ci gaban tattalin arzikinmu,” in ji Tinubu wanda ya kai ziyarar kwanaki uku a Faransa ga taron.
“Wannan, zan jaddada, shine dalilin da ya sa muke buƙatar ƙwararrun Faransa da masu zuba jari da su ƙara yin aiki a wannan fanni don taimakawa wajen bunƙasa yawan matasan mu.”
Ya ce Nijeriya na ƙoƙarin karkatar da tattalin arzikinta daga gurɓataccen man fetur kuma yana ganin Faransa za ta iya taka muhimmiyar rawa a wannan matakin.
“Muna da damar da za mu iya karkatar da tattalin arzikinmu daga albarkatun mai,” in ji shi.
“A Legas, alal misali, mun horar da Tekun Atlantika zuwa yanzu kuma muna ci gaba da inganta tattalin arzikin ruwa. Kamun kifi wani muhimmin ɓangare ne na ƙarfin tattalin arzikinmu,” in ji shi.
Shugaba Tinubu ya gode wa gwamnatin Faransa bisa samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwan Nijeriya a ƙasar ta Turai.
“Na gode da samar da yanayi mai kyau don bunƙasa su kuma muna samar da hanya guda don zuba jari a cikin tattalin arzikin Nijeriya don ‘yan ƙasar Faransa a fannin samar da abinci,” in ji Tinubu.
Nijeriya ita ce kan gaba wajen samar da man fetur a Afirka kuma tana da masana’antar fina-finai mai ƙarfi, wadda ake yiwa laƙabi da “Nollywood”.
Tinubu ya ce har yanzu ƙasar na buƙatar ƙara yin aiki tare da ƙasar Faransa a wannan fanni.
“Najeriya a shirye take ta haɗa gwiwa da Faransa domin mu samu ingantaccen aikin tsaro wanda zai dakatar da hijira,” in ji shi, yana mai ƙara jaddada buƙatar samar da yanayi na lumana na kasuwanci.
Macron, mai shekaru 46, wanda ya nemi “sabuntawa” tsakanin Paris da Afirka tun bayan zaɓensa na 2017, ya ce ƙasarsa za ta “ci gaba da saka hannun jari” a Nijeriya, a daidai lokacin da tasirin Faransa a nahiyar ke raguwa bayan juyin mulkin soja.
Ziyarar Tinubu ita ce ziyarar aiki ta farko da wani jigo a Nijeriya ya kai sama da shekaru ashirin.
