Adamu Ibrahim Wanki ya zama Daraktan Ma’aji na FCTA

Spread the love

An naɗa Alhaji Adamu Ibrahim Wanki a matsayin sabon Daraktan Ma’aji na Hukumar Birnin Tarayya, Abuja.

Wanki ya zama sabon Daraktan ne biyo bayan ritayar da mai riƙe da muƙamin, Alhaji Zanna Hamza, ya yi a sakamakon cika shekara 60 da ya yi a bakin aiki.

Bikin miƙa ragamar ofishin ya gudana ne a babban zauren taron sashen tsarin tattalin arziƙi da ƙididdiga na FCTA da ke area 11, Abuja.

Taron ya samu halartar daraktoci na sassa daban-daban haɗi da sauran jami’an FCTA.

Kafin naɗin nasa, Alhaji Adamu Ibrahim Wanki shi ne jami’i mafi girma a sashen nasu.

Sashen ma’ajin FCTA shi ne sashen da ke kula da sha’anin kuɗi na hukumar wanda kulawar kuɗaɗen shiga na ciki da waje da akan tara ke ƙarƙashinsa.

By Editor