Wike ya ɗora alhakin yajin aikin malaman Abuja kan shugabannin ƙananan hukumomi

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya zargi shugabannin kananan hukumomin shida da laifin yajin aikin da malaman makarantun firamare ke cigaba da yi a yankin.

Wike, wanda ya yi wa ’yan jarida jawabi a ranar Talata a Abuja jim kadan kafin wani taron gaggawa da hukumomin tsaro, ya ce jami’an kananan hukumomin ba su cika aikin da aka dora musu ba.

A ranar Lahadin da ta gabata ne Kungiyar Malamai ta babban birnin tarayya Abuja ta umurci malaman firamare da su shiga yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar 15 ga watan Janairu.

Yajin aikin dai an dara ne inda inda aka tsaya bayan na farko da kungiyar ta dakatar a shekarar 2023 kan rashin biyan kashi 40 cikin 100 na alawus da kuma karin albashi na watanni 25 da dai sauransu.

NUT ta dakatar da yajin aikin ne a ranar 2 ga Oktoba, 2023 don ba da damar warware matsalolin cikin makonni shida, amma ba a yi komai ba.

Don haka ministan ya dora alhakin yajin aikin da aka dade ana yi a kan shugabannin, sannan ya bukace su da su kara kaimi wajen gudanar da ayyukansu.

By Editor