Gwamnatin Nijeriya ta yi Allah wadai da yadda aka yi wa Super Eagles, ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasa, a lokacin da aka tsare su a filin jirgin sama na Al Abraq na Libya na tsawon awanni.
Super Eagles sun tafi Libya don wasan neman gurbin AFCON na 2025 a zagaye na biyu tare da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Libya.
Sai dai, a lokacin tafiyar, jirgin da ke ɗauke da Super Eagles da wakilan hukumar ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) ya canza hanya zuwa wani wuri.
Hukumar Libya ta tsare Super Eagles a filin jirgin sama, ta hana su zuwa inda suka nufa.
Wata sanarwa daga Sashen harkokin watsa labarai na NFF a ranar Litinin ta bayyana cewa, ƙungiyar ta samu rashin kulawa a filin jirgin sama na Al Abraq.
Wani bidiyo da ƙungiyar Super Eagles ta wallafa ya tabbatar da wannan al’amari, inda ‘yan wasa da jami’ai, tare da kayansu, aka bar su a filin jirgin sama, yayin da jami’an filin jirgin na Libya suka yi watsi da matsalar su.
Duk da haka, sabbin bayanai daga NFF sun ce Super Eagles ba za su yi wasan neman gurbin AFCON na 2025 da Libya ba sakamakon wannan wahala da suke ciki.
A yayin da yake mayar da martani ga wannan al’amari, Ministan Wasanni, John Enoh, ya ce ya tura rahoton rashin kulawa da aka yi wa Super Eagles daga hukumomin Libya tun bayan isowarsu a filin jirgin sama na Al Abraq ranar Lahadi.
Enoh ya ce ya sanar da dukkan hukumomin da suka dace game da wannan lamari.
Ya kuma ce a halin yanzu, babban burin shine tsaron tawagar ’yan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasa.
