Gwamnatin Jigawa za ta fara hukunta masu yin ba-haya a bainar jama’a

Spread the love

Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse

Gwamnatin Jihar jigawa tace za ta Gina banɗakuna a kasuwanni da tashohin mota, a ƙoƙarinta na yaƙi da ba-haya a bainar jama’a da wasu ke yi.

Kwamashinan ruwa na jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa ya bayyana haka a wajen bikin ranar tsafta da wanke hannu ta duniya da ya gudana a makarantar kiwon lafiya ta Jahun.

Kakakin Majalisar dokokin jihar Alh. Haruna Aliyu Ɗan Gyatin ya wakilci Gwamna Umar Namadi a yayin taron ƙaddamar da banɗakuna da Hukumar Albarkatun Ruwa ta gina a makarantar.

Hannun Giwa ya ce irin waɗannan banɗakuna, gwamnati ta samar da guda 35 a wasu manyan makarantun jihar a ƙoƙarin tare da hukumar da nufin inganta yanayin tsaftar muhalli.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ita ce ta ɗaya a Nijeriya wajen hana yin ba-haya a bainar jama’a.

Ya kuma ce tuni gwamnatin ta ɗauki matakan hana yin ba-haya barkatai a faɗin jihar ciki har da kasuwanni da tashoshin mota, sannan sunan sa ran nan da wata biyu, doka za ta fara aiki masu irin wannan aiki na ɓata muhalli.

By Babaji