EFCC ta bankaɗo makarantar koyon yahoo a Edo

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin ƙasa Ta’annati (EFCC), ta ce ta kama mutane 25 waɗanda take zargin masu damfara ne ta yanar gizo a wani wuri da ake kyautata zaton na horar da damfara ne a Benin, babban birnin Jihar Edo.

A cikin wani rubutu da ta ɗora a shafinta na X, hukumar ta ce ta yi nasarar yin hakan ne a ranar Alhamis ta hanyar amfani da jami’anta na Benin.

Ta ce kamen ya biyo bayan samun wasu sahihan bayanan sirri ne da ke nuna cewa ana amfani da wani gini a matsayin wurin koyar da damfarar yahoo ko kuma horar da masu son ƙwarewa a sauran hanyoyin damfara ta intanet.

BBC Hausa ta ruwaito cewa, EFCC ta ce ta kuma gano wasu kaya a lokacin samamen nata, waɗanda suka haɗa da dalla-dallan motoci guda shida, da kwamfutoci da kuma wayoyi.

“Nijeriya dai ta yi ƙaurin suna a harkar damfara ta intanet a duniya”, kamar yadda BBC Hausa ta wallafa a shafinta na Facebook.

By ukarofi