Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya mayar da martani kan rahoton cewa ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris, ya yi watsi da kalamansa dangane da sake dawowar hare-haren Boko Haram a jihar.
Zulum a baya ya bayyana cewa ‘yan Boko Haram da ISWAP sun fara sake kai hare-hare da sace mutane a yankin, kuma cewa dakarun tsaro ba su nuna isasshen martani ba, lamarin da ya sa ya nuna damuwa kan taɓarɓarewar tsaro.
Sai dai wata sanarwa daga hadimin minista Idris, Rabiu Ibrahim, ta musanta wannan, tana mai cewa ministan bai taba cewa a yi watsi da Zulum ba ko ya ce Boko Haram ba ta dawowa ba. Sanarwar ta kira rahoton da aka yaɗa “ƙarya ce kuma an shirya shi don tada hankali.”
Amma a wani sabon jawabi da Zulum ya yi wa manema labarai a ranar Asabar, ya ce:
“Ba na son shiga gardama da ministan, amma ina ganin bai san me ke faruwa a ƙasar nan ba. A ganina, bai da cikakken sani.”
Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba za ta yi shiru ba yayin da Boko Haram ke sake samun ƙarfi, kuma za su haɗa gwiwa da sojoji da jami’an tsaro domin hana wannan.
Zulum ya ce sun riga sun gana da manyan hafsoshin tsaro a Abuja, ciki har da shugaban hafsoshin tsaro, rundunar sojin ƙasa, ruwa da sama, kuma sun samu tabbacin cewa za a ɗauki matakai masu ƙarfi.
A ƙarƙashin jagoranci na, Boko Haram ba za ta sake samun damar da ta samu a baya ba, in sha Allah. Za mu ƙarfafa JTF, mafarauta da bijilante sosai. Ba za mu yi watsi da wannan barazana ba,” in ji Zulum.
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da goyon baya ga sojojin Najeriya domin tabbatar da zaman lafiya da daƙile sake tasowar Boko Haram.
