Kotu a Amurka ta dakatar da yunƙurin Trump na korar baƙin haure 500,000

Spread the love

Wata alkali a ranar litinin ɗin da ta gabata ta hana gwamnatin shugaba Donald Trump na Amurka yin gaggawar soke matakin shari’a na dubban daruruwan bakin haure daga Venezuela, Cuba, Nicaragua da Haiti.

Hukuncin da mai shari’a Indira Talwani ta yanke a birnin Boston shi ne umarni na baya-bayan nan kan yunƙurin da Trump ya yi cikin gaggawa na gudanar da korar jama’a, musamman ga ‘yan Latin Amurka.

A watan Maris, gwamnatin ta ce tana shirin soke matsayin doka na wasu ‘yan Cuba, Haiti, Nicaragua da kuma Venezuelan 532,000 da suka zo Amurka a ƙarƙashin wani shirin “parole” wanda tsohon shugaban ƙasar Joe Biden ya kaddamar a watan Oktoba 2022.

Talwani ta rubuta a cikin odar ta ta: “Kotu ta ba da agajin gaggawa don dakatar da Kashe Tsare-tsaren kora ga baƙi a Cuban, Haiti, Nicaraguans, da Venezuelans.”

Shirin ‘parole’ ya ba da damar shiga Amurka na tsawon shekaru biyu ga bakin haure 30,000 a kowane wata daga ƙasashen huɗu, waɗanda ke da munanan bayanan hakkin ɗan adam.

A cikin umarninta, Talwani, ta ce gwamnatin Trump ta yi aiki da wata mummunar fassara ta dokar shige da fice, tare da gaggauta tsige waɗanda ba ‘yan asalin ƙasar ba da suka shiga Amurka ba bisa ƙa’ida ba, amma ba waɗanda aka ba da izinin zama a ƙasar ba, kamar dai waɗanda ke ƙarƙashin shirin.

A ƙarƙashin hukuncin na Trump, baƙin hauren sun rasa kariyarsu ta doka daga ranar 24 ga Afrilu, kwanaki 30 kacal bayan da Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida ta buga odar a ƙarƙashin umurin gwamnatin Tarayya.

Trump ya sha alwashin korar miliyoyin ‘yan ci-rani da ba su da takardun izini a wa’adinsa na biyu, bayan gudanar da yaƙin neman zaɓe da ya mayar da hankali kan shige da fice ba bisa ƙa’ida ba.

Daga cikin wasu matakan, ya kafa dokar da kai tsaye ta bada umurnin jigilar daruruwan mutanen da ake zargi da kasancewa mambobin wata ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Venezuela zuwa El Salvador, da ke daure.

By ukarofi