Bologna ta lashe gasar kofin Italiya a ranar Laraba bayan da ta doke AC Milan da ci 1-0 a birnin Rome kuma ta kawo ƙarshen shekaru 51 da ta shafe tana jiran lashe babban kofi.
Dan wasa Ndoye ne ya zura ƙwallon a minti na 53 da fara wasan wanda ya baiwa Bologna nasara mai cike da tarihi, wanda kuma shi ne karramawar da suka samu tun bayan lashe kofin ƙarshe a shekarar 1974.
Bologna ba ta ma shiga babbar gasa ta ƙarshe ba tun bayan da ta lashe kofin Italiya na ƙarshe – karo na biyu a gasar kofin gida biyu.
Amma koci Vincenzo Italiano ya yi kyakkyawan aiki tun lokacin da ya zo ya maye gurbin Thiago Motta a Bologna, wanda ya lashe gasar Italiya sau bakwai amma ya yi hakan a 1964.
Nasarar Laraba kuma ita ce babbar karramawa ta farko da Italiano ya samu a matsayin koci yayin da ya yi rashin nasara a wasanni uku na ƙarshe a kulob ɗinsa na baya wato Fiorentina, ciki har da gasar kofin Italiya ta 2023.
Italiano ya rungumi ‘yan wasansa masu murna yayin da magoya bayan Bologna ke rawa da kuka a filin wasa na Olimpico bayan sun ga abin da mutane da yawa ke tunanin ba za su taba gani ba.
