2027: APC ta gargaɗi Ndume kan kalamansa na kamanta faɗuwar Goodluck da takarar Tinubu ta biyu

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI

Jam’iyyar APC ta yi gargaɗi ga tsohon mai tsawatarwa a Majalisar Dattawa, Sanata Ali Ndume, bisa kalamansa na cewa akwai yiwuwar irin yadda tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Johnathan ya gaza koma wa mulki a karo na biyu, ya faru da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Ta ce, duk da cewa tana maraba da ra’ayoyi mabanbanta, haka kuma tana da hanyoyin ladabtar da mambobinta da suka saɓa wa dokokinta.

A wata hira da Daraktan yaɗa labaranta, Bala Ibrahim ya yi da manema labarai a ranar Litinin, ya ce APC jam’iyya ce da ke karɓar ra’ayoyi da dama ba tare da kawo tsaiko ba.

A ranar Lahadi ne Ndume ya bayyana kalaman nasa ta gidan talabijin na Channels, inda ya ce matuƙar Tinubu bai ɗauki darasi ba daga faɗuwar Johnathan a zaɓen 2015 ba, akwai yiwuwar shi ma ya rasa nasara a zaɓen 2027.

A shekara 2015 ne Jonathan, wanda shi ne Shugaban ƙasa a lokacin, ya rasa damar koma wa kujerar bayan da Muhammadu Buhari na APC ya doke shi.

Buhari ya samu ƙuri’u 15,424,921, a yayin da Johnathan ya zo na biyu da ƙuri’u 12,853,162.

Lamarin da ya sa a karon fari a tarihin Nijeriya aka samu shugaba mai mulkin da ya rasa damar komawa a karo na biyu.

By Babaji