An yanke wa tsohon soja hukuncin rataya kan laifin fashi

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Wata Babbar Kotu a Jihar Akwa-Ibom ta yanke wa wasu ƴan fashi guda biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun su da laifin fashi ga wasu ƴan adaidaita sahu a babban birnin jihar, Uyo.

Ɗaya daga cikin su shi ne Lance Corporal Promise Okokon Usoro, wanda tsohon soja ne da aka sallame shi a aiki daga bataliya ta 6 ta rundunar sojojin Nijeriya dake Barikin Ibagwa a Ƙaramar Hukumar Abak.

Usoro mai shekaru 41, an same shi ne da bindiga ƙirar AK-47 da laifin yin fashi ga wani mai suna Peter Daniel Okon inda ya ƙwace masa babur ɗinsa mai taya uku bayan yi masa barazana da bindiga a daren ranar 10 ga watan Fabarairun 2013.

Da fari, an same shi ne da laifin saɓa wa aikin soja, lamarin da ya sa aka sallame shi a aiki tare da damƙa ga ƴan sanda domin gurfanar da shi a kotu.

Tuni Usoro ya masa laifin yin fashi sau uku ga masu adaidaita sahu a birnin Uyo tare da taimakon wani da ake kira da JJ wanda shi ma a yanzu yana hannu.

By Babaji