Daga GAMBO ISA a Abuja
ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Bayo a majalisar dokokin jihar Borno kuma shugaban kwamitin majalisar kan muhalli Hon. Maigari Maina Abare, ya taya mataimakin shugaban tarayyar Nijeriya Sanata Kashim Shettima murnar zagayowar ranar haihuwarsa da aka yi kwanan nan.
A cikin saƙon fatan alheri da aka raba wa jaridar Blueprint a Abuja, Hon. Abare ya bayyana mataimakin shugaban ƙasa Shettima a matsayin shugaban da ya tsayu kai da fata wajen gina alaƙa da haɗin kai da fahimtar juna a faɗin ƙasar nan.
Ya yi nuni da cewa jagoranci na siyasa da falsafar shugabanci na mataimakin shugaban ƙasa ya zaburar da sabbin shugabannin masu hangen nesa a ciki da wajen jihar Borno.
“Matakin nasihar siyasa da mai girma Sanata Kashim Shettima ya yi, abin a yaba ne matuƙa. Jagorancin sa ya ci gaba da tsarawa tare da ƙarfafa fagen siyasar Nijeriya,” Hon. Abare ya bayyana.
ɗan majalisar ya ƙara yaba wa mataimakin shugaban ƙasa Shettima bisa rawar da yake takawa wajen tantancewa da kuma ba da jagoranci nagari irin su Gwamna Babagana Umara Zulum, wanda ya bayyana a matsayin “mutumin da ya dace a daidai wurin da ya dace” da yake tafiyar da al’amuran jihar Borno cikin himma da ƙwazo.
Hon. Abare ya kuma yaba da kafa hukumar raya yankin arewa maso gabas (NEDC), mai hedikwata a Maiduguri, ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa Shettima da kuma goyon bayan Shugaba Ahmed Bola Tinubu, wanda kwanan nan ya ƙirƙiro ma’aikatar raya yankin domin ƙarfafa ci gaban yankin.
Ya yaba da ƙwarin gwiwar da aka samu ga hukumar alhazai ta ƙasa a ƙarƙashin kulawar mataimakin shugaban ƙasa, inda ya jaddada inganta tsarinta da riƙon amana.
Hon. Abare ya yi amfani da wannan dama wajen yin kira ga matasa da dattawan ƙaramar hukumar Bayo ta jihar Borno da ma al’ummar ƙasa baki ɗaya da su ci gaba da zama a dunƙule, su yi wa ƙasa addu’a, su ci gaba da zama ‘yan’uwansu na zaman lafiya da ci gaba.
Ya kuma yaba wa Sarkin Biu da Shehun Borno bisa yadda suke ci gaba da jagoranci na uba da nasiha mai kyau wajen wanzar da zaman lafiya da ci gaba a yankunansu.
Da yake ƙarƙare saƙonsa, Hon. Abare ya miƙa saƙon taya murna ga mataimakin shugaban ƙasa Shettima: “Ina fatan ranarku ta musamman ta cika da farin ciki, ƙoshin lafiya, hikima, da ci gaba da samun nasara a hidimarku ga babbar al’ummarmu,” ya ce.
