Gwamnatin Amurka ta bayyana cewa ta kama Shugaban Venezuela, Nicolás Maduro, a wani mataki da ya ƙara tayar da ƙura a siyasar duniya, musamman a yankin Latin Amurka. Hukumomin Amurka sun ce an kai Maduro New York domin fuskantar shari’a a kotun tarayya bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi da ta’addanci.
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya tabbatar da kama Maduro, inda ya ce an gudanar da aikin ne cikin tsari mai tsauri, ba tare da asarar rayuka ba. A cewarsa, jami’an tsaro sun fuskanci ƙalubale masu yawa kafin samun nasarar kama shugaban.
A cewar Ma’aikatar Shari’ar Amurka, tuhumar da ake yi wa Maduro ba sabuwa ba ce. Tun a shekarar 2020 ne gwamnatin Amurka ta zarge shi da jagorantar wata ƙungiyar safarar hodar iblis wadda ke aiki tare da ‘yan tawayen FARC na Colombia, da nufin shigar da miyagun ƙwayoyi cikin Amurka.
Hukumomin sun ce za a tantance ko za a ƙara masa wasu tuhume-tuhume, ko kuma a ci gaba da shari’ar bisa tuhumar da ke akwai. An kuma tunatar da cewa Amurka ta taɓa sanya ladar maƙudan kuɗi kan duk wanda ya taimaka wajen kama Maduro.
Bayan sanarwar kama shugaban, gwamnatin Venezuela ta yi kakkausar suka, tana kiran matakin a matsayin cin mutuncin ikon ƙasa. Mataimakiyar Shugaban ƙasar, Delcy Rodríguez, ta nemi Amurka da ta bayyana a hukumance inda Maduro yake da kuma halin da yake ciki.
A lokaci guda, jami’an tsaro a Venezuela sun ƙara tsaurara matakan tsaro a manyan birane, yayin da gwamnati ke kira ga jama’a da su kasance masu kwantar da hankalinsu.
ƙasashe da dama sun nuna damuwa kan lamarin. Rasha da Iran sun yi Allah-wadai da matakin, suna cewa hakan ya saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa. A ɗaya ɓangaren kuma, Tarayyar Turai ta buƙaci dukkan ɓangarori da su yi aiki da hankali tare da mutunta dokokin duniya.
Rasha ta ce aikin Amurka wani “aikin ƙiyayya ne na makami” kuma ta yi kira ga tattaunawa don guje wa ƙarin tashin hankali.
Iran ta yi Allah-wadai da farmakin a matsayin gagarumin keta ƙa’idar `yanci da cikakken iko na ƙasa.
ƙasashen Latin Amurka kamar Brazil, Meɗico, Chile da Colombia sun bayyana cewa farmakin ya saɓa wa dokar duniya kuma ya zama haɗari ga zaman lafiya a yankin.
Majalisar ɗinkin Duniya (UN) ta nuna damuwar cewa farmakin ya kafa “mummunan misali” ga amfani da ƙarfin soja a duniya kuma ta buƙaci hukumomi su bi ƙa’idar Dokar UN.
Tarayyar Turai (EU) kuma ta yi kira ga a guji ƙara tashin hankali tare da wajabta girmama ƙa’idodin doka da zaman lafiya.
A sauran ƙasashen duniya kuwa wannan hukuncin na Amurka ya samu mabambanta ra’ayoyi, inda wasu ke ganin dagewar haka kamar yadda wasu suka faɗi akasin hakan.
A Argentina, shugaban ƙasa Javier Milei ya bayyana cewa matakin ya kawo ƙarshen mulkin wanda ya ƙi bin ƙa’idodin demokraɗiyya, don haka labari ne mai kyau ga “duniya mai ‘yanci”.
A cikin Amurka ma, wasu ‘yan siyasa sun saka alamar tambayoyi kan tushen doka da kuma rawar da Majalisa ta taka a wannan mataki.
Masu sharhi sun lurar da cewa wannan lamari na kama shugaban ƙasa yana tuna wa da abin da ya faru a shekarar 1990, lokacin da Amurka ta kama Manuel Noriega, tsohon shugaban Panama, lamarin da ya sauya akalar siyasar ƙasar a wancan lokaci.
Kama Nicolás Maduro ya buɗe sabon babi a rikicin da ke tsakanin Amurka da Venezuela, babi da ke ɗauke da tambayoyi masu yawa kan ikon ƙasa, doka da makomar yankin.
Zuwa yanzu dai duniya ta sa ido, tana jiran ganin inda wannan lamari zai dosa da irin tasirin da zai yi ga zaman lafiya a yankin.
