Jamiyyar PDP a Gombe sun yi maraba da Bargan Gombe gabanin zaɓen 2027

Spread the love

Daga ABUBAKAR A BOLARI GOMBE

Harkokin siyasa a Jihar Gombe na ƙara ɗaukar zafi gabanin zaɓen shekarar 2027, inda manyan jiga-jigan jam’iyyar PDP a mazaɓar Gombe ta Arewa suka tarbi Hon. Sadeeq Abubakar Gidado, PhD, Bargan Gombe, a wani taron tattaunawa da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa da matakin ƙasa na jam’iyya.

An gudanar da taron ne a sakatariyar PDP ta ƙaramar hukuma da ke Gombe, inda shugabannin mazaɓu da wakilai daga yankuna shida Shamaki, Ajiya, Nassarawo, Bajoga, Dawaki da Herwagana suka halarta.

A jawabinsa, Bargan Gombe ya bayyana cewa ziyarar na daga cikin matakan tuntuɓa da yake yi da shugabannin jam’iyya, domin bayyana burinsa na siyasa da kuma karɓar shawarwari daga matakin da ke da kusanci da jama’a.

Ya ce matakin tsayawa takara ya samo asali ne daga ƙarfafawa da kuma matsin lamba daga magoya baya da jama’a, inda ya ƙara da cewa ƙungiyar siyasa mai suna Kogunan Gombe ta nuna goyon baya ta hanyar sayen fom ɗin takararsa.

Bargan Gombe ya jaddada cewa babu wata nasara ta siyasa da za a iya samu ba tare da gina tushe a matakin mazaɓu ba, yana mai cewa shugabannin gunduma su ne ginshiƙin kowace tafiyar jam’iyya.

Ya ce: “Idan ba a fara aiki daga ƙasa ba, ba za a iya gina ingantacciyar nasara a siyasa ba. Waɗannan shugabanni su ne ke kusa da jama’a kuma su ne ke jagorantar fahimtar al’umma.”

A nasu ɓangaren, shugabannin mazaɓar PDP sun yi maraba da ziyarar, suna masu bayyana ta a matsayin abin a yaba da ke nuna girmamawa ga tsarin jam’iyya da dimokuraɗiyya ta cikin gida.

Sun kuma bayyana Bargan Gombe a matsayin ɗan siyasa mai tasiri da kuma alaƙa mai ƙarfi da matakin ƙasa, tare da masa fatan alheri da nasara a tseren zaɓen 2027.

An kammala taron cikin yanayin haɗin kai da fahimtar juna, inda ɓangarorin suka sha alwashin ci gaba da haɗin gwiwa yayin da siyasa ke ƙara ɗaukar sabon salo a jihar.

By ukarofi