Babbar Sallah: Zulum ya sanya takunkumin zirga-zirga a Borno

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Gwamnatin Jihar Borno ta sanar da sanya takunkumin zirga-zirgar ababen hawa da mutane na wucin-gadi domin tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da sallar Idi a gobe Laraba.

Rahotanni sun bayyana cewa, takunkumin, wanda Gwamna Babagana Zulum ya amince da shi, zai fara aiki ne daga ƙarfe 6 na safe zuwa 11 na safe a ranar Laraba. Haka kuma, zai shafi motoci, adaidaita sahu da babura.

Matakin na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Rundunar Sojin Nijeriya ta yi gargaɗin yiwuwar hare-haren ta’addanci a wuraren taruwar jama’a a faɗin jihar.

A sanarwar da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Tsaron Cikin Gida, Usman Tar ya fitar, ya ce an ɗauki matakin ne domin ƙara inganta tsaro a yayin bikin sallah da al’umma ke gudanar da shungulla.

Ya yi kira ga mazauna jihar da su gudanar da sallah a filayen Idi mafi kusa da gidajensu domin sauƙaƙa zirga-zirga da kuma taimakawa jami’an tsaro wajen tantance jama’a cikin sauki.

A cewar sanarwar, jami’an tsaro, motocin ɗaukar marasa lafiya, jami’an kashe gobara da sauran ma’aikatan da ke gudanar da muhimman ayyuka tare da sahihin katin shaida, takunkumin bai shafe su ba.

By Babaji