Kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa ya yi tsokaci kan yiwuwar komawa gasar firimiyar Nijeriya.
Musa ya buƙaci magoya bayansa da su yanke shawara a kan ƙungiyar da zai kasance a cikin ƙungiyoyi 20 na NPFL.
Tsohon ɗan wasan NPFL ya bayyana hakan a shafukan sada zumunta.
Musa ya rubuta a kan ɗ tare da tambarin ƙungiyoyin NPFL 20: “In sake komawa, wanne ƙunhiya ku ke so in sanya hannu a wannan a ciki.”
A baya Musa ya buga wasanni biyu da Kano Pillars a NPFL.
ɗan wasan mai shekaru 31 ya kasance ba shi da kulob tun bayan da ya bar kulob ɗin Siɓasspor na Turkiyya.
