
Daga BELLO A. BABAJI
Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya jinjina wa Hukumar Haɗaka ta Kula da bada Gurbin karatu (JAMB), bisa nasarar da ta samu a yayin aikin jarrabawar UTME da ke gudana ta hanyar amfani da komfuta, wato CBT.
Ya ce, daga watan Nuwamban 2025 ne za a fara gudanar da jarrabawar WAEC da NECO ta tsarin CBT kamar yadda ake yi a yayin rubuta na JAMB.
A yayin sanya ido kan jarrabawar UTME a Ƙaramar Hukumar Bwari dake Birnin Tarayya Abuja ne Ministan ya ce, rubuta jarrabawar ta CBT zai taimaka wajen yaƙar satar amsa, wanda a saboda haka ne ya kafa kwamiti da zai samar da tsarin rubuta jarrabawa mai inganci ga ɗalibai a Nijeriya.
Dakta Tunji ya yaba da tsarin CBT da ya gani a cibiyoyin hukumar daban-daban a Nijeriya yayin da ɗalibai suke rubuta jarrabawa, lamarin da ya ce ɗaya ne daga cikin ababen da za su taimaka wajen inganta al’umma, kamar yadda ya ke a tsarin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Ya ƙara da cewa, jarrabawar WAEC da NECO da za yi a watannin Mayu da Yunin 2026 za a yi su ne baki ɗaya ta komfuta, saɓanin a takarda da ake yi baya.
A cewarsa, hakan zai taimaka wajen samar da nagartattun ɗalibai da za su yi gogayya da sauran ɗalibai a kowane mataki na karatu s duniya.
