Ambaliya: An yi sabon gargaɗi ga wasu jihohin arewa

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta gabatar da sabon gargaɗi ga jihohin arewa guda tara sakamakon yiwuwar samun mamakon ruwan sama a tsakanin ranakun 25 da 29 ga watan Agusta, 2025, lamarin da ka iya haddasa ambaliya a garuruwa da dama.

Daraktan Reshen kula da lamuran ambaliya da yankuna masu barazanar ambaliya a Ma’aikatar Muhalli, Usman Abdullahi Bokani ya bayyana haka a wata takarda, ranar Litinin a Abuja.

A cewar sanarwar, Cibiyar Gargaɗin Ambaliya Akan lokaci (FEW Centre) ta bayyana sassan wasu jihohi a matsayin wuraren da ka iya fuskantar gagarumar ambaliya.

Jihohin sune; Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Sakkwato da Zamfara.

Bokani ya kuma ce, garuruwan suna halin fuskantar mamakon ruwan sama a ƴan kwanakin nan, don haka akwai buƙatar ɗaukar matakan kariya domin kauce wa iftila’in.

Ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a jihohin da lamarin ya shafa da su kasance a ankare, sannan su riƙa aiko da rahoto akai-akai ta yadda za a shawo kan matsalar yayin da ta ke ƙoƙarin tunkarar yankunan.

Ga wasu daga cikin sassan a jihohi kamar haka:

Adamawa: Mubi, Shelleng, Abba-Kumbo

Katsina: Katsina, Kaita, Bindawa

Jigawa: Gwaram

Gombe: Nafaɗa

Borno: Ngala

Kano: Sumaila

Zamfara: Anka

Sakkwato: Makira

Bauchi: Azare da Jama’are.

By Babaji