APC ta tsayar da ranakun zaɓen fidda gwani

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Jam’iyyar APC mai mulki ta bayyana ranakun 30 da 31 ga Mayu ranakun da za ta yi zaɓen fidda wanda zai cira tutar jam’iyyar a zaɓen Shugaban Ƙasa da ke tafe a 2023.

Sakataren jam’iyyar, Iyiola Omisore, ne ya saka hannu a takardar wanda jam’iyyar ta aika wa hukumar zaɓe.

Idan ba a manta ba hukumar zaɓe ta umarci jam’iyyun ƙasar nan su tabbata sun yi zaɓen fidda gwani da kuma aika wa da sunayen yan takarar kujerun su a farkon watan Yuni.

APC ta ce za ta gudanar da zaɓen kujeran gwamna a jihohi da na majalisar jihohi a ranakun 23 da 11 ga Mayu.

Wato na gwamna ranar 23, na ‘yan majalisar jiha kuma ranar 11 ga Mayu. Za a yi zaɓen fidda gwani na kujerun majalisar tarayya da na dattawa ranar 18 ga Mayu.

Jam’iyyar za ta gudanar da babban taron ta a ranar Laraba mai zuwa wanda shine taro na farko da za ta yi a ƙarƙashin sabbin zaɓaɓɓun shugabannin ta wanda aka yi a watan Maris.

Idan ba a yi samu jituwa tsakanin ‘yan takaran jam’iyyar musamman kujerar shugaban ƙasa ba, to ko za a yi kare jini, biri jini a wajen zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasar.

Babban dalilin haka kuwa shine ganin jigajigan jam’iyyar da dama sun fito takarar kujerar shugaban ƙasa.

Waɗanda za a fafata a tsakanin su kuwa sun haɗa da Bola Tinubu, Rotimi Amaechi, Rochas Okorocha, David Umahi, Orji Uzor Kalu, Yahaya Bello, da mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo da dai sauran su.

By Editor