22
Jun
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta ce, makirce-makircen da Jam’iyyar APC mai mulkin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ke yi na ƙwace Jihar Ribas da ƙarfin tsiya ya kai intaha na ƙoƙarin ƙwace jihar da ƙarfin tsiya daga PDP, amma ta ce hakan ba zai cimma nasara ba. A ranar Laraba ne shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Ribas suka buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci a jihar, bisa zargin cewa jihar na cikin yanayin tashin-tashina. Shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar APC, Tony Okocha ne ya yi wannan kiran a yayin wani taron manema…
