ukarofi

11226 Posts
Yadda Gwamnatin Tarayya ta bankaɗo ma’aikatan bogi da suke zaune a ƙasashen waje 

Yadda Gwamnatin Tarayya ta bankaɗo ma’aikatan bogi da suke zaune a ƙasashen waje 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Dakta Folasade Yemi-Esan, Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, HOCSF, ta ce aikin tantance ma'aikata da ofishinta ya yi kwanan nan, ya bankaɗo ma’aikatan da ke zaune a ƙasashen waje kuma har yanzu suna samun albashi daga Nijeriya. Yemi-Esan ta bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ta yi da shugabannin kafafen yaɗa labarai a ranar Laraba a Abuja, kasancewar wani ɓ angare na ayyukan bikin Makon Ma’aikata na 2024. Taken bikin na 2024 shi ne 'Koyar da Ƙwararriyar Afirka don Ƙarni na 21: Gina Tsarukan Ilimin Juriya don Ƙarfafa Samun Haɗuwa, Tsawon Rayuwa, Inganci da…
Read More
Jihar Kogi za ta ɗauki mafarauta 1,000 aikin tsaro

Jihar Kogi za ta ɗauki mafarauta 1,000 aikin tsaro

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin jihar Kogi na shirin ɗaukar 'yan sa-kai 1,050 da zimmar kyautata tsaron jihar da ke tsakiyar Nijeriya. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa an ɗauki matakin ne bayan majalisar dokokin jihar ta amince da buƙatar da gwamnati ta gabatar mata yayin zamanta na ranar Laraba. Tun da farko, Kwamashinan Ƙananan Hukumomi Salami Ozigi-Deedat ya aika wa majalisar wasiƙar neman amincewarta na ɗaukar mafarauta 50 daga kowace ƙaramar hukuma 21 na faɗin jihar. Gwamnatin ta bayyana ƙarancin jami'an tsaro a matsayin babban dalilin ɗaukar mafarautan aiki. Bayan amincewar da suka yi,…
Read More
Sufeton ‘yan sandan Nijeriya ya tura ƙarin dakaru Ribas bayan kisan ɗan sanda

Sufeton ‘yan sandan Nijeriya ya tura ƙarin dakaru Ribas bayan kisan ɗan sanda

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sufeto janar na 'yan sandan Nijeriya ya yi tir da kisan jami'n rundunar da aka yi a jihar Ribas sakamakon rikicin siyasar da ke ci gaba da ruruwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da tsohon Gwamna Nyesom Wike. Wata sanarwa da kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce IGP Kayode Egbetokun ya bai wa kwamashinan 'yan sandan jihar umarnin tsaurara tsaro don gano waɗanda suka aikata kisan. Sanarwar ta ce an kashe Sufeto Daɓ id Mgbada da kuma wani ɗan sa-kai Samuel Nwigwe a rikicin da ya auku tsakanin magoya ɓ angarorin biyu bayan…
Read More
Maiduguri na cikin birane mafiya tsaro a Nijeriya – Janar Christopher Musa

Maiduguri na cikin birane mafiya tsaro a Nijeriya – Janar Christopher Musa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hafsan Hafsoshin Nijeriya, Janar Christopher Musa, ya ce Maiduguri babban birnin jihar Borno na daga cikin wurare mafiya tsaro a Nijeriya a halin yanzu duk da rikicin Boko Haram da birnin ya yi fama da shi a baya. Janar Musa ya bayyana haka ne a ranar Laraba lokacin da yake ganawa da shugabannin kafofin yaɗa labarai a Abuja. Ya ce: "Mutane ne kawai suke ganin kamar babu tsaro a Maiduguri, amma birnin na daga cikin waurare mafiya tsaro a ƙasar yanzu haka”. Babban hafsan tsaron na Nijeriya ya ce rundunar sojin ƙasar ta yi…
Read More
Muna fuskantar matasalar ƙarancin kayan marmari a Gombe – Dauda Wanke

Muna fuskantar matasalar ƙarancin kayan marmari a Gombe – Dauda Wanke

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe 'Yan kasuwar kayan marmari sun koka da ƙarancin kayan a wannan lokaci wanda rashin kayan ya sa sun koma kamar 'yan zaman banza domin ƙarancin  kayan ya sa sun shiga ruɗu. Dauda Malam Wanke wani mai sana'ar kayan marmari da ke sayar da kayan akan babbar hanyar zuwa gidan gwamnati a fadar jihar, ya koka matuƙa inda ya ce kayan ya yanke kuma ya yi tsada wanda suna ji suna gani sun zama Allah Sarki. Ya ce abinda ya jawo rashin kayan shi ne lokacin sa ya yanke kuma wani bai fito ba kuma…
Read More
Tsarin tafiyar Kwankwasiyya na kula da bunƙasa ci gaban al’umma daga tushe – Dahiru Arrow

Tsarin tafiyar Kwankwasiyya na kula da bunƙasa ci gaban al’umma daga tushe – Dahiru Arrow

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano  An bayyana cewa al'ummar Jihar Kano sun gamsu da takun gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf bisa la'akari da irin muhimman  ayyuka da ya gudanar cikin shekara ɗaya da kama mulki shi ya sa suke mara masa baya. Babban mai taimakawa Gwamnan Jihar Kano akan harkar tsaftar muhalli, Hon. Ɗahiru Arrow Dakata ne ya bayyana haka da yake zantawa da 'yan jarida a yayin taron bikin Sallah da aka gudanar ba harabar gidan jagoran Kwankwasiyya Dakta Rabiu Musa Kwankwaso. Ya ce duk mutumin da yake a cikin tsarin tafiyar Kwankwasiyya musamman  gwamnati al'ummar…
Read More
Masu dukan mata ku tuba ku daina!

Masu dukan mata ku tuba ku daina!

Kwanaki wata marubuciya ta yi wani rubutu a shafinta na manhajar Facebook, inda ta bayyana takaicinta game da halayyar wasu azzaluman maza da ke cin zarafin matansu ta hanyar duka, abin da ya jawo muhawara mai zafi daga ɓangarori daban-daban, sakamakon yadda wannan mummunar halayya ke ci musu tuwo a ƙwarya. Mata da dama, musamman masu aure, suna kokawa da yadda wasu mazan ke kasa daurewa fushi da ɓacin ransu, da zarar matansu sun musu wani kuskure ko laifi sai su hau jibgarsu kamar jakuna, ba mutane ba. Wani lokaci ma idan abin ya zo da tsautsayi har lahani ake…
Read More
Kano Civil Society Forum ta rantsar ta sabbin shugabanninta bayan shekara 11

Kano Civil Society Forum ta rantsar ta sabbin shugabanninta bayan shekara 11

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gamayyar ƙungiyoyin fararen hula ta Kano wato Kano Civil Society Forum (KCSF) ta rantsar da sabbin shugabannin da za su gudanar da ƙungiyar bayan shekara 11 a ƙarƙashin tsarin shugabancin riƙo. Jaridar Blueprint Manhaja ta ruwaito cewa taron rantsarwar ya gudana ne a cibiyar ‘yan jarida ta NUJ da ke Kano a ranar Talata da ta gabata.  Sabon Shugaban gamayyar Muhammad Bello, wanda kuma shi ne shugaban cibiyar binciken ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban Afirka wato African Center For Innoɓatiɓe Research and Deɓelopment ya ce ya na mai gode wa ƙungiyar bisa wannan aiki da aka…
Read More
Za a fara ɗaukar masu takardun HND a matsayin malamai a Kwalejin Kimiyya da Fasaha – Bugaje

Za a fara ɗaukar masu takardun HND a matsayin malamai a Kwalejin Kimiyya da Fasaha – Bugaje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Yanzu haka dai waɗanda suka mallaki Babbar Difloma ta Ƙasa (HND) za a ɗauke su a matsayin malamai a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a ƙarƙashin sabbin tsare-tsaren aiki, kamar yadda Babban Sakataren Hukumar Kula da Ilimin Fasaha ta Ƙasa (NBTE), Farfesa Idris Mohammed Bugaje ya sanar. Ya yi wannan jawabi ne a ranar Larabar da ta gabata yayin gabatar da sabbin tsare-tsaren aiki ga masu ruwa da tsaki a fannin kimiyyar ƙere-ƙere, kamar yadda shugabar ma’aikata, Dakta Folasade Yemi-Esan ta amince da shi. Ya ce a cikin sabbin tsare-tsare, an soke Malaman makarantar da…
Read More
Aƙalla mutum 21 sun mutu, yayin da 401 suka kamu da Kwalara a Legas

Aƙalla mutum 21 sun mutu, yayin da 401 suka kamu da Kwalara a Legas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Adadin waɗanda suka mutu sakamakon ɓarkewar cutar Kwalara a Legas a ranar Alhamis ya kai 21, inda ake zargin mutane 401 sun kamu da cutar a faɗin jihar. Mataimakiya ta musamman ga gwamnan jihar Legas kan harkokin kiwon lafiya, Dr. Kemi Ogunyemi da ke yin ƙarin haske kan cututtuka, ta bayyana cewa adadin masu ɗauke da cutar Kwalara ya ƙaru zuwa 401 a faɗin Legas, inda Legas Island, Kosofe, da Eti Osa suka fi yawa. Ogunyemi, yayin da take bayani kan ɓullar cutar bayan ta gana da jami’an hukumar bayar da agajin gaggawa ta…
Read More