21
Jun
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu ya saduda, inda ya bayyana cewa a shirye yake ya tattauna da wakilan gwamnati. Kanu ya bayyana hakan ne a cigaba da shari’ar da mai shari’a Binta Nyako ta babbar kotun tarayya da ke Abuja ke jagoranta. Shugaban ƙungiyar ta IPOB ɗin dai yana hannun Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) tun a shekarar 2021 inda aka sake kama shi tare da dawo da shi domin ci gaba da shari’ar sa bisa zarginsa da laifin ta'addanci da cin amanar ƙasa. Sai dai a zaman da aka cigaba da sauraron ƙarar…
