Ba Gwamnatin Tarayya kaɗai ke da haƙƙin kula da al’umma ba – MURIC

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Kungiyar Kare Muradun Musulman Nijeriya (MURIC) ta buƙaci ‘yan Nijeriya su mayar da hankalinsu kan gwamnonin jihohi maimakon mayar da hankali kacokan kan matsalolin ƙasar ga Gwamnatin Tarayya.

A sanarwar da ta fitar albarkacin bikin cika shekara 64 da samun ‘yancin Nijeriya, ƙungiyar ta ce idan har ana son tabbatar da shugabanci nagari har sai an riƙa sa ido kan gwamnonin jihohi.

“A kullum ‘yan Nijeriya na taƙaita buƙatunsu ne kan gwamnatin tarayya yayin da kuma galibin buƙatun na kan wuyan gwamnonin jihohi. An rarraba haƙƙin tsakanin jihohi 36,” a cewar sanarwar da shugaban MURIC, Ishaƙ Akintola ya fitar a ranar Talata.

Kungiyar ta nuna cewa sa ido kan gwamnoni zai ƙara tabbatar da gaskiya da adalci wanda kuma zai tabbatar da kyakkyawan shugabanci a Nijeriya wanda zai tilasta wa gwamnoni sauke haƙƙin da ke wuyansu.

’Yan Nijeriya a kodayaushe suna takaita sha’awarsu ga ayyukan gwamnati zuwa cibiyar alhalin ba a ajiye dukiyar al’ummarmu a cibiyar ita kaɗai. An raba shi a tsakanin dukkan jihohi 36. Don haka abu ne mai ban mamaki koyaushe a yi tsammanin fayyace gaskiya, gaskiya da riƙon amana a cibiyar kaɗai. Za mu ci gaba da neman shugabanci na gari har sai mun fara sa ido a kan gwamnonin jahohi da kuma ɗora su a kai.

By ukarofi