Ban damu ba don wata rana wani gwamna ya cire ni – Sarki Sanusi

Spread the love

Alhaji Muhammadu Sanusi II, sarkin kano na 16 yace ba zai damu ba don wata gwamnatin ta zo ta cire shi ba.

Tsohon Gwamna Abdullahi Gamduje ya tsige Sanusi saboda wani matsala dake tsakanin su.

Yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara naɗa Sarki Sanusi, Sarkin kano na 15 Aminu Ado ya garzaya Kotu domin Ƙalubalantar cirewar.

Yayin da yake ganawa da jaridar Saturday Sun, Sarki Sunusi ya ce, bai san tsawon lokacin da zai daɗe a kan karagar mulkin.

Ya ƙara da cewa, shi kansa da yake kai yanzu, Allah ne kaɗai ya san lokacin da zai kai kan karagar tunda zan iya mutuwa ko wanne lokaci. Ko kuma wani Gwamna yazo ya cire ni wannan ba zai dameni ba.

Sai dai zan so kar ya cire ni sabida bana so ace lokaci na ne tarihin sama da shekaru 1000 ya lalace.

A shekara huɗu da suka wuce, ba wai ina zaune hake kawai ne ba, domin in gab da kammala digiri na uku a jami’ar Landan.

By ukarofi