Rahoto

Hukumar gidan gyaran hali ta ziyarci Sarkin Kabin Argungu

Hukumar gidan gyaran hali ta ziyarci Sarkin Kabin Argungu

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Hukumar gidan gyaran hali reshen ƙaramar hukumar Argungu ƙarƙashin jagorancin babban Sufurtanda Lauwal Yeldu ta ziyarci fadar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama'ila Muhammad Mera. Da ya ke jawabi yayin ziyarar Yeldu ya bayyana irin nasarorin da gidan da ke reshen ƙaramar hukumar Argungu ya samu a ƙarƙashin jagorancinsa sun haɗa da kimanin mutane ashirin suka sauke Al’ƙur’ani Maigirma, aƙalla sama da mutane arba'in sun koyi sana'o'in hannu daban-daban tare da samun ƙwarewa a cikin sana'o'in da suka haɗa da ƙere-ƙere da saƙe-saƙe wanda yanzu haka wadansu daga cikin su sun cigaba da sana'o'in…
Read More
Tsarin siyasa ne ya lalata makomar Nijeriya, inji Sarki Sanusi

Tsarin siyasa ne ya lalata makomar Nijeriya, inji Sarki Sanusi

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya zargi manyan 'yan siyasar Nijeriya da gaza yi wa ƙasa aiki, yana mai cewa suna naushin cigaban al’umma ta hanyar fifita kansu a kan buƙatun jama’a. Sarkin na wannan jawabi ne a bikin cika shekaru 15 da kafuwar Enough is Enough (EiE) Nigeria a Lagos, ranar Laraba, Sanusi ya bayyana cewa Nijeriya na ci gaba da rasa muhimman damar bunkasuwa saboda yadda wasu ke ɗaukar muƙaman gwamnati a matsayin “gadon gidansu"  amanar al’umma ba. A cewarsa, yawancin shugabannin siyasa suna sa buƙatunsu da na iyalansu a gaba fiye da…
Read More
Tasirin zagin malamai ga tarbiyyar ‘ya’ya

Tasirin zagin malamai ga tarbiyyar ‘ya’ya

Daga AISHA ASAS Kafin na kai ga darasin namu na yau wanda yake da matuƙar tasiri a wannan zamani da muke ciki, zan soma kan shimfiɗa kan ita kanta ɗabi'a ta zagin malamai. Aya a cikin littafi mai tsarki ta cikin surar Al-An'am, aya ta 153. Allah Maɗaukacin sarki Ya ce, "Kuma lallai wannan ce hanya ta madaidaiciya, ku bi ta, kada ku bi 'yan hanyoyi, za su rarraba ku daga bin hanyaTa........." A wani hadisi da ba zan iya tuna ko daga wa ta fito ba, sahabbin ya ce, "Alokacin da manzon Allah yake karanta wannan ayar, yana zaune…
Read More
Harshen Hausa da Hausawa, bayyanarsu da yaɗuwarsu (I)

Harshen Hausa da Hausawa, bayyanarsu da yaɗuwarsu (I)

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kamar yadda muka faɗa a makon da ya gabata cewa, za mu riƙa kawo wa mai karatu Tarihin manyan ƙabilun Nijeriya. A yau za mu bayyana taƙaitaccen asalin tarihin Hausawa a Nijeriya. ƙabilar Hausa dai ƙabilace da ke zaune a arewa maso yammacin tarayyyar Nijeriya da kudu maso yammacin Jamhuriyyar Nijar, ƙabilace mai ɗimbin al’umma, amma kuma a al'adance mai mutuƙar haɗaka, aƙalla akwai sama da mutane miliyan hamsin da harshen yake asali gare su. A tarihi an ce ƙabilar Hausawa na tattare a salasalar ko manyan birane. Hausawa dai sun sami kafa daularsu ne tun…
Read More
Pharmacist Ahmed Ibrahim Yakasai: Jagora mai gina al’umma ya cika shekaru 65

Pharmacist Ahmed Ibrahim Yakasai: Jagora mai gina al’umma ya cika shekaru 65

Daga KABIR SAIDU DANLADI FUNTUA A cikin duniyar da ake buƙatar shugabanni masu hangen nesa, ɗabi’a, da kishin mutane, akwai wasu mutane da fitilarsu ba ta gushewa. A Najeriya musamman a fannin kiwon lafiya, irin wannan haske ya bayyana ta fuskar Pharmacist Ahmed Ibrahim Yakasai — Wanda taimako da tallafinsa sun haɗa fannoni da yawa tun daga ilimi, jagoranci, alheri, kasuwanci, da bauta wa al’umma. An haife shi a 1 Ga watan Disamba, 1960, kuma tun Yana dan karami ya fara karatun Allo, Islamiyya da karatun zamani. daga wannan lokacin ya fara tafiyar da ta zamo ginshiƙi ga dubban mutane.…
Read More
Sheikh Dahiru Bauchi: Ya kwanta dama bayan shekaru 101 masu albarka (1346AH – 1447AH)

Sheikh Dahiru Bauchi: Ya kwanta dama bayan shekaru 101 masu albarka (1346AH – 1447AH)

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Cikin mutane sama da biliyan takwas da suke raye a wannan duniya tamu a yau, kimanin mutane 722,000 a cikinmu sun sami tsawon rai na kai wa shekaru 100 cif. To idan zan yi la’akari da wannan ma’aunin kawai, zan iya cewa hakika Marigayi Sheikh Dahiru Bauchi, na daya daga cikin mutane da Allah ya yi wa wata kebabbiyar baiwa kasancewar ya shiga cikin jerin wadannan mutane da su ka rayu tsawon shekaru dari a duniya. Na tabbatar kuma idan za’a sake wata kididdigar a cikin wadancan mutane masu shekaru dari a duniya, Shehin dai, zai…
Read More
Dalilin da ya sa ake banƙarewa budurwa leɓe a ƙabilar Kibishi

Dalilin da ya sa ake banƙarewa budurwa leɓe a ƙabilar Kibishi

Su dai waɗannan bayin Allah suna rayuwa ne a yammacin kogin ‘Omo’ da ke kudu-maso-yammacin Habasha, ana kiransu da ‘Kibishi’. Bincike ya nuna cewa su dai waɗannan mutane makiyayane, sannan a kan gane yawan dukiyar kowane gida ta hanyar la’akari da yawan dabbobin da suka mallaka. Addini: Waɗannan mutane suna da abin bauta wanda suke yi masa laƙabi da ‘Tuma’. Sun yi imani cewar shi dai wannan Tuma ya kasancene a cikin sararin samaniya, bugu da ƙari mutanen sun yi imani da al’matsutsai da kuma ifiritai, sun kuma yi imani da cewar su ɗin a karan kansu na iya sanya…
Read More
Kungiyar masana zane-zane ta koka kan gobarar da ta laƙume Herwa Heart of Art Gallery

Kungiyar masana zane-zane ta koka kan gobarar da ta laƙume Herwa Heart of Art Gallery

Daga WAKILINMU Sanannen wajen koyar da fasaha na Herwa Heart of Art Gallery, wacce ta shahara a matsayin babban cibiyar ƙirƙira kuma ta samu lambar yabo ta Outstanding Gallery Award daga ƙungiyar ɗaliban Zane-Zane ta Nijeriya (SNA), ta ƙone ƙurmus a ranar Juma’ar da ta gabata sakamakon abin da shaidun gani da ido suka bayyana a matsayin fashewar hasken rana kwatsam. Wannan lamari ya tayar da hankulan maƙota da ke yankin. Akan haka ne ƙungiyar SNA ta bayyana al’amarin a matsayin babban rashi ba ga 'yan ƙungiyar ba kaɗai har ma ga ɗalibai masu tasowa, asarar a matsayin babbar rashi…
Read More
Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP ta sace a Borno

Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP ta sace a Borno

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sojojin Operation Hadin Kai sun ceci ’yan mata 12 da ake zargin mayakan ISWAP ne suka sace a yankin Mussa da ke ƙaramar hukumar Askira/Uba a Jihar Borno. An sace ’yan matan ne a ranar 23 ga Nuwamba yayin da suke aikin girbi a gonakinsu. Harin ya sanya mazauna yankin da dama tserewa zuwa makwabtan ƙauyuka. A cewar majiyoyin tsaro da jaridar Zagazola Makama ta fannin yaki da ta’addanci ta rawaito, an gudanar da aikin ceton ne a ranar Asabar. Har yanzu ba a tabbatar ko an biya kuɗin fansa ba. An 'yan matan…
Read More
Gwamnatin Nasarawa za ta kafa ‘yan sandan jiha

Gwamnatin Nasarawa za ta kafa ‘yan sandan jiha

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnatin jihar Nasarawa ta bayyana shirinta na kafa rundunar ‘yan sandan jiha idan kundin tsarin mulkin ƙasar ya amince da hakan. Kalaman sun fito ne daga kwamishinan tsaro da harkokin sauran al’amura, CP Usman Baba yayin wani taron manema labarai a Lafia, babban birnin jihar. Kwamishinan ya ce tun daga zuwan gwamnatin jihar a 2019, an fifita harkar tsaro, tare da ba rundunonin tsaro tallafi na ababen hawa da kayan aiki da sauran kayan aikace-aikace. Ya jaddada cewa gwamna Abdullahi Sule ya ƙuduri aniyar tabbatar da cewa jihar ta kasance amintacciya ga masu zuba…
Read More